Kurunkus: Dangote Ya Fadi Dalilin da Ya Sa Ake Sayan Fetur da Tsada a Najeriya
- Aliko Dangote ya ce farashin fetur a ƙasashen makwabta ya fi na Najeriya da kashi 30 zuwa 50 cikin 100, lamarin da ke ƙarfafa fasa-kwaurinsa
- Ya ce a Nijar, farashin fetur ya fi na Najeriya da kashi 20 zuwa 25 cikin 100, wanda ke ba masu fasa-kwauri damar samun riba cikin sauri
- Dangote ya bayyana cewa wasu ’yan kasuwa na iya karkatar da fetur da ake nufin sayarwa a Najeriya zuwa kan iyaka domin sayar da shi a ƙasashe makwabta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Legas - Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya danganta tsadar fetur a Najeriya da wasu dalilai, ciki har da ci gaba da fasa-kwaurin man zuwa ƙasashe makwabta.
Dangote ya ce farashin fetur a ƙasashen da ke makwabtaka da Najeriya ya fi na cikin gida da kashi 30 zuwa 50 cikin 100, lamarin da ke ba masu safarar man zuwa ƙetare babbar damar samun riba.

Kara karanta wannan
Dangote ya yi maganar samun yaron da zai gaje shi, ya fadi fatansa kan 'ya'yansa mata 3

Source: Getty Images
Dangote ya bayyana hakan ne a wata hira da tashar Arise News da aka watsa ranar Talata, 15 ga watan Satumban 2026.
Me Dangote ya ce kan tsadar fetur?
Dangote ya ce ba za a iya kallon farashin fetur a Najeriya shi kaɗai ba tare da kwatanta shi da farashin da ake sayar da shi a ƙasashe makwabta ba.
“Ka sani, tsada abu ne na kwatance. Abin da ya kamata su yi shi ne su tambayi kansu, nawa ne farashin fetur a ƙasashe makwabta?” in ji shi.
Ya ce har yanzu ana fasa-kwaurin man fetur da ake samarwa a Najeriya zuwa ƙasashen da ke makwabtaka da ƙasar.
Abin da ke sa fasa-kwauri
A cewar Dangote, bambancin farashin fetur tsakanin Najeriya da ƙasashe makwabta na ƙara ƙarfafa masu safarar man zuwa ƙetare.
Ya ce mutumin da ya sayi fetur a Najeriya zai iya kai shi wata ƙasa makwabciya ya sake sayar da shi kan farashi mafi girma.

Kara karanta wannan
"Ba na son a kara kira na wanda ya fi kowa kudi a Afrika"; Dangote ya fadi sunan da yake so
“Ban sani ba ko kun san cewa har yanzu ana fasa-kwaurin fetur ɗin da muke samarwa zuwa ƙasashe makwabta,” in ji shi.
Dangote ya ce idan farashin fetur a makwabciya kasa ya fi na Najeriya da kashi 30 zuwa 50 cikin 100, hakan yana samar da babbar damar samun riba.
Dangote ya yi misali da Nijar
Dangote ya kawo misalin Nijar, inda ya ce farashin fetur ya fi na Najeriya da kusan kashi 20 zuwa 25 cikin 100.
Ya ce idan ana sayar da litar fetur a Najeriya kan N1,350, farashinsa a Nijar na iya zama sama da na Najeriya.
“Mutane za su iya tambaya, idan yanzu farashin N1,350 ne, to nawa ne a Nijar? Farashin Nijar ya fi na Najeriya da kashi 20 zuwa 25 cikin 100,” in ji shi.
Ya tambayi irin kasuwancin da mutum zai iya yi wanda zai ba shi riba mai yawa cikin gaggawa.
“Wane irin kasuwanci za ka yi da zai ba ka riba kashi 25 cikin 100 nan take?” Dangote ya tambaya.

Source: Facebook
Dangote ya yi maganar samun magaji
A wani labarin kuma, kun ji cewa Aliko Dangote, ya ce samun ɗa namiji da zai gaji daular kasuwancinsa ba shi ne babban abin da ya fi ba muhimmanci ba.
Hamshakin attajirin ya ce ’ya’yansa mata uku, Halima, Fatima da Mariya, suna da ƙwarewar da za ta ba su damar jagorantar kasuwancin Dangote Group.
Asali: Legit.ng
