Alkawarin Obi ga Kwankwaso kan Wa'adi 1 Ya Ci Gaba da Jawo Rudani a Arewa
- Yarjejeniyar wa'adi ɗaya tsakanin Peter Obi da Rabiu Kwankwaso ta fara jawo rarrabuwar kai a Arewa
- Ƙungiyar ACF ta ce yarjejeniyar alamar neman mulki ne cikin gaggawa, yayin da wasu suka ce ya dace da tsarin karɓa-karɓar mulki tsakanin yankuna
- Lauyoyi sun bayyana cewa kundin tsarin mulki bai amince da irin yarjejeniyar ba, don haka ba ta da ƙarfin doka kuma ba za ta tilasta kowa ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Ana ci gaba da maganganu game da tikitin dan takarar shugaban kasa a NDC, Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso.
Yarjejeniyar da Peter Obi, ya kulla da abokin takararsa Sanata Rabiu Kwankwaso na yin wa'adi ɗaya idan ya lashe zaɓe ya jawo muhawara daga ƙungiyoyin Arewa da manyan lauyoyi.

Source: Facebook
Kwankwaso ya tabbatar a wata hira da Channels Television cewa Obi ya rattaba hannu kan yarjejeniya a rubuce, wadda ta tanadi mika mulki ga Arewa bayan wa'adi ɗaya.
Obi ya yi alƙawarin yin wa'adi guda ɗaya kacal domin mutunta tsarin karɓa-karɓar mulki tsakanin Arewa da Kudu, ganin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana mulki daga Kudu.
Tsohon gwamnan Kano ya bayyana cewa yana da cikakken yaƙini Obi zai cika alƙawarinsa, yana mai cewa sun yi wannan yarjejeniya ne cikin amana da mutunta juna.
Sai dai ƙungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta yi watsi da yarjejeniyar, tana mai cewa ba ta da tushe a kundin tsarin mulki kuma alamar matsananciyar neman mulki ce.
Sakataren yaɗa labarai na ACF, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya ce babu wanda ya ba Obi ko Kwankwaso ikon tattauna makomar shugabancin Najeriya tsakanin Arewa da Kudu.
A cewarsa, idan Obi ya zama shugaban ƙasa kuma ya yi aiki nagari, babu abin da zai hana shi neman wa'adi na biyu saboda kundin tsarin mulki ya ba shi damar hakan.
A gefe guda, ƙungiyar Middle Belt Forum (MBF) ta ce ba ta da matsala da alƙawarin wa'adi ɗaya, muddin hakan zai ba yankin Middle Belt damar karɓar mulki a shekarar 2031.
Mai magana da yawun MBF, Luka Binniyat, ya ce tun farko sun goyi bayan ci gaba da mulki a Kudu zuwa 2031, sannan daga baya shugaban ƙasa ya fito daga Middle Belt.
Ƙungiyar ta kuma yi iƙirarin cewa tun 1999 Arewar Musulmi ta samu damar mulki sosai, don haka lokaci ya yi da ɗan takarar Kirista daga Middle Belt zai jagoranci ƙasar.
Manyan lauyoyi da suka yi magana kan batun sun ce irin wannan yarjejeniya ba ta da ƙarfin doka, domin kundin tsarin mulkin Najeriya ya amince da wa'adin shekara huɗu da damar yin wa'adi biyu.
Babban lauya Abdul Balogun (SAN) ya ce doka ba ta tanadi irin wannan yarjejeniya ba, yayin da Hillary Omoh ta ce kowanne ɓangare na iya janye ba tare da hukunci ba.
Shi ma lauya James Ekwe ya ce duk wanda ya rattaba hannu kan irin wannan yarjejeniya zai dogara ne da mutuncinsa wajen cika alƙawarin, domin babu wata doka da za ta tilasta hakan.
Asali: Legit.ng

