"Ba Kushe ba": Shugaban APC, Nentawe Ya ba 'Yan Adawa Shawara ana Shirin Zaben 2027
- Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bukaci 'yan adawa su daina sukar gwamnati kawai
- Farfesa Nentawe Yilwatda ya ce ya kamata 'yan siyasa su gabatar da ingantattun hanyoyin magance kalubalen tattalin arzikin Najeriya
- Yilwatda ya ce cire tallafin man fetur ya zama wajibi domin ceto tattalin arzikin kasar daga durkushewar kasafin kudi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bukaci shugabannin 'yan adawa su daina sukar gwamnati kawai.
Farfesa Nentawe ya bukaci su mayar da hankali wajen gabatar da ingantattun hanyoyin magance kalubalen tattalin arzikin Najeriya.

Source: Facebook
Yilwatda ya yi wannan kira ne a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan kafafen yada labarai da dabarun yada bayanai, Abimbola Tooki, ya fitar ranar Alhamis, 23 ga watan Yulin 2026, cewar rahoton jaridar Daily Trust.
An fitar da sanarwar ne bayan kammala bikin cin abincin dare na bayar da lambobin yabo ga Majalisar Dokoki ta Kasa karo na 10 da aka gudanar a Abuja.
Da yake magana ta bakin wakilinsa, Daniel Rejenieju, shugaban APC na kasa ya bukaci 'yan siyasar adawa su daina yin Allah wadai da manufofin gwamnati kawai, su kuma bayar da gudunmawa mai ma'ana wajen ci gaban kasa.
Dalilin cire tallafin man fetur
Ya ce cire tallafin man fetur da gwamnatin APC karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta yi, mataki ne da babu makawa kuma ya zama dole domin ceto tattalin arzikin Najeriya daga durkushewar kasafin kudi da ke gabatowa.
Shugaban jam'iyyar na kasa ya bayyana tsarin tallafin da ake yi a baya a matsayin wanda ba zai dore ba, yana mai cewa ya amfanar da wasu tsirarun masu gata ne kawai, yayin da ya hana kasar kudaden da take bukata domin muhimman ayyukan ci gaba.
Ya bukaci 'yan Najeriya su ci gaba da nuna goyon baya ga sauye-sauyen tattalin arziki masu muhimmanci da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa.
Nentawe ya kwantar da hankulan 'yan Najeriya
Farfesa Yilwatda ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa wahalhalun da ake fuskanta na dan lokaci sakamakon sauye-sauyen za su kawo karshen su, tare da samar da ci gaban tattalin arziki mai dorewa, daidaiton kasafin kudi da kuma wadata da za ta amfanar da kasa baki daya.
"Kalubalen tattalin arziki da ake fuskanta a yanzu sakamako ne na dan lokaci na sauye-sauyen da aka tsara domin gyara matsalolin tsarin da suka dade suna addabar kasa," in ji Yilwatda
Ya kara da cewa Shugaba Tinubu ya nuna kudurin kawo gyara da gwamnatocin da suka gabata suka kasa nunawa, jaridar Vanguard ta kawo labarin.

Source: Facebook
Shugaban APC ya gana da Kabiru Gaya
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kai ziyarar girmamawa ga jigon jam'iyyar NDC a Kano, Sanata Kabiru Gaya.
Farfesa Nenatwr Yilwatda ya bayyana cewa tattaunawar da suka yi ta fi mayar da hankali ne kan haɗin kan al'ummar Kano da kuma buƙatar shugabanni su ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna.
Asali: Legit.ng

