'An Gama Komai': Ƴan Arewa Sun Tabbatar wa Tinubu Nasara a Zaɓen 2027

'An Gama Komai': Ƴan Arewa Sun Tabbatar wa Tinubu Nasara a Zaɓen 2027

  • Ƙungiyar North Central Agenda (NCA) ta fadi yadda za ta taimaka wurin tabbatar da nasarar Bola Tinubu a 2027
  • Ta bayyana goyon bayanta ga sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu a 2027, tana mai cewa nasararsa a yankin ta zama tabbaci
  • Kungiyar ta ce gwamnatin Tinubu ta kawo manyan ayyukan tituna, ilimi, noma da tsaro, lamarin da ya inganta rayuwar al'ummar Arewa ta Tsakiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Ƙungiyar North Central Agenda (NCA) ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Ƙungiyar ta jaddada cewa za ta ba da gudummawa domin ya sake neman wa'adi na biyu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

An ƙarfafawa Tinubu guiwa kan zaben 2027
Shugaba Bola Tinubu yana jawabi a taro. Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Source: Twitter

Shugaban ƙungiyar, Ene Ogbole, ta bayyana hakan ne yayin wani taron kwana guda da aka gudanar a Abuja, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

ADC ta nemi gwamnati ta fito da bayanai kan yadda aka kashe N17.5tr a NNPCL

Tabbacin da ƙungiya ta ba Tinubu

Ogbole ya ce tattaunawa na ci gaba a yankin Arewa ta Tsakiya ƙarƙashin manufar Renewed Hope ta gwamnatin Tinubu.

Ƙungiyar ta ce nasarar shugaban a yankin Arewa ta Tsakiya ta riga ta zama abin da ba za a iya sauyawa ba.

Ogbole ta kuma yi watsi da sabon cece-kuce kan tikitin Musulmi da Musulmi na jam'iyyar APC, tana mai cewa 'yan Najeriya sun riga sun yanke hukunci a kan batun tun lokacin babban zaɓen shekarar 2023.

Ta ce kafin gwamnatin Tinubu ta hau mulki a watan Mayun 2023, yankin Arewa ta Tsakiya ya dade yana fama da ƙarancin manyan ayyukan raya ƙasa da kuma matsalolin tsaro.

A cewarta, manufofin gwamnatin sun samar da sabon fata ta hanyar saka hannun jari a manyan tituna, noma, ilimi da tsaro, wanda ya haifar da ci gaba mai anfani ga yankin.

Ta lissafa manyan ayyuka kamar hanyar Calabar–Ebonyi–Benue–Kogi–Nasarawa–Abuja, hanyar Sokoto–Badagry, hanyar Akwanga–Jos–Bauchi–Gombe–Maiduguri, hanyar Suleja–Minna da kuma aikin faɗaɗa hanyar Lokoja–Okene a matsayin muhimman ayyukan da ke amfani yankin.

Kara karanta wannan

ADC ta fadi yadda za ta kawo karshen mulkin Tinubu a 2027

Kungiya ta goyi bayan zaben Tinubu a 2027
Shugaba Bola Tinubu na Najeriya. Hoto: Bayo Onanuga.
Source: Facebook

Ayyukan alheri da Tinubu ya yi

A cewarta, yadda gwamnatin Bola Tinubu ta raba ayyukan raya ƙasa cikin adalci a dukkan shiyyoyin Najeriya ya sauya yanayin yankin daga rashin kulawa zuwa ci gaban tattalin arziki da manyan ayyukan more rayuwa.

Saboda haka, ta ce ƙungiyar za ta tattara gagarumin goyon baya a dukkan jihohin Arewa ta Tsakiya shida da Babban Birnin Tarayya domin tabbatar da sake zaɓen Tinubu a shekarar 2027.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, wanda Babatunde Benard ya wakilta, ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke yi suna shimfiɗa tubalin bunƙasar Najeriya na dogon lokaci.

Ya ce shugaban yana ɗaukar matakai masu wahala amma masu muhimmanci domin gyara tattalin arzikin ƙasa, duk da cewa sakamakonsu ba zai bayyana nan take ba.

Gwamna ya fadi tasirin Tinubu kan sauran takwarorinsa

Mun ba ku labarin cewa Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya ce Shugaba Bola Tinubu ya fi sauran masu neman takarar shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

An sako Tinubu a gaba ya yi murabus kafin zaben 2027 bayan rahoton Bankin Duniya

Abdullahi Sule ya ce banbancin da ke tsakanin Tinubu da abokan hamayyarsa ya yi kama da dare da rana.

Gwamnan ya bayyana ayyukan raya ƙasa, ilimi da ci gaban kasuwar hannayen jari a matsayin nasarorin gwamnatin Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.