A Karshe, Peter Obi Ya Bar Boye Boye, Ya Fadi dalilin Daukar Kwankwaso Mataimakinsa

A Karshe, Peter Obi Ya Bar Boye Boye, Ya Fadi dalilin Daukar Kwankwaso Mataimakinsa

  • Peter Obi ya ce ya fadi dalilin zabar Sanata Rabiu Kwankwaso a matsayin abokin takararsa a zaben shekarar 2027
  • Obi ya musanta jita-jitar sabani tsakaninsa da Kwankwaso, yana mai cewa suna aiki tare domin samar da sauyin da zai inganta rayuwar 'yan Najeriya
  • Dan takarar NDC ya ce haɗa magoya bayan Obidient da Kwankwasiyya ba zai haifar da rikici ba, domin burinsu ɗaya ne na ceto Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Dan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC mai adawa a Najeriya, Peter Obi, ya yi karin haske kan dalilin daukar Rabiu Kwankwaso.

Peter Obi ya bayyana cewa ya zaɓi Rabiu Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa na zaɓen 2027 saboda suna da manufa iri ɗaya ta yaƙi da talauci ta hanyar ilimi da bunƙasa tattalin arziki.

Kara karanta wannan

An sako Tinubu a gaba ya yi murabus kafin zaben 2027 bayan rahoton Bankin Duniya

Obi ya fadi dalilin daukar Kwankwaso a matsayin mataimaki
Dan takarar shugaban kasa a NDC, Peter Obi da mataimakinsa, Rabiu Kwankwaso. Hoto: Mr. Peter Obi.
Source: Facebook

Musabbabin alakar Obi da Kwankwaso

A wata hira da jaridar The Sun ta wallafa, Obi ya ce haɗin gwiwarsu ya samo asali ne daga ƙimomi iri ɗaya da kuma hangen nesa na sake gina Najeriya.

Ya jaddada cewa su biyun sun fi mayar da hankali kan kawo sauyi mai amfani fiye da siyasar anfani ta kashin kai.

Tsohon gwamnan Anambra ya ce Kwankwaso ya daɗe yana ba ilimi da bunƙasa jarin ɗan Adam muhimmanci, kuma hakan ya yi daidai da shirinsa na farfaɗo da Najeriya.

Obi ya ce:

"Kwankwaso yana da falsafar fitar da mutane daga talauci. Ni ma haka nake. Ya yi imani da ilimi, domin ba za a sauya al'umma ba tare da ilimi ba."

Ya ƙara da cewa ilimi ne zai kasance ginshiƙin manufofinsa, domin shi ne hanyar sauya al'umma da gina jarin ɗan Adam da Najeriya ke buƙata domin ci gaba.

Kara karanta wannan

'Amfanin da soke ba da tallafin Amurka zai yi ga Najeriya' in ji Jigon APC

Obi ya karyata maganar sabani tsakaninsa da Kwankwaso
Dan takarar shugaban kasa a NDC, Peter Obi. Hoto: Mr. Peter Obi.
Source: UGC

Obi ya yi karin haske kan 'sabani' da Kwankwaso

Obi ya kuma musanta rahotannin da ke cewa akwai saɓani tsakaninsa da Sanata Rabiu Kwankwaso.

Ya ce bai san dalilin da ya sa ake yaɗa irin waɗannan jita-jita ba, domin ba a taɓa ganin su suna rikici ba.

A cewarsa, matsalolin siyasa na samo asali ne daga shugabanci mai anfani ta kashin kai, yayin da shi da Kwankwaso suke son shugabanci mai kawo sauyi wanda zai fitar da mutane daga talauci tare da inganta rayuwarsu.

Peter Obi ya bayyana cewa shi da Kwankwaso sun haɗu a ƙarƙashin jam'iyyar NDC bayan rikice-rikicen cikin gida da shari'o'i da suka dabaibaye ADC, inda suka yanke shawarar kafa sabon dandamalin siyasa domin tunkarar zaɓen 2027.

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ba su haɗa kai kafin zaɓen 2023 ba, Obi ya ce ba ya son komawa baya, domin hankalinsa yana kan makomar Najeriya da abin da zai amfani al'umma.

Kara karanta wannan

An daure yar TikTok kan yada cewa shugaban kasa ya birne shanu 32 don cin zabe

Ya kuma yi watsi da fargabar cewa haɗa magoya bayan Obidient da Kwankwasiyya zai haifar da rabuwar kai. A cewarsa, dukkan bangarorin suna da buri iri ɗaya na ganin an samu sabuwar Najeriya mai ci gaba da walwalar jama'a.

Buba Galadima: "Akwai Kalubale kan Tikitin Obi, Kwankwaso"

An ji cewa jigo a jam'iyyar NDC, Buba Galadima ya ce ana fuskantar ƙalubale wajen tabbatar da tikitin haɗin gwiwar Peter Obi da Rabiu Kwankwaso a 2027.

Ya yi wannan jawabi ne jim kadan bayan bayanan da ya yi a baya game da dalilan da suka jawo aka hada kai tsakanin manyan yan siyasar.

Injiniya Buba Galadima ya kuma buƙaci a daina ɗora wa Peter Obi laifin juyin mulkin soja na shekarar 1966 da aka yi a kasar nan saboda ba hannunsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.