Peter Obi Ya Bayyana Yiwuwar Haƙura da Neman Takarar Shugaban Kasa, Ya Kawo Dalili
- Ɗan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi ya ce akwai yiwuwar ba zai sake neman takarar shugaban kasa ba bayan zaben 2027
- Tsohon gwamnan na jihar Anambra ya danganta hakan da tsarin karba-karba na mulkin Najeriya tsakanin Arewa da Kudu
- Obi ya ce idan mulki ya koma Arewa a 2031, zai kai shekara 78 kafin damar ta sake dawowa Kudancin Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Ɗan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi, ya bayyana cewa akwai yiwuwar ba zai sake neman kujerar shugaban kasa ba bayan babban zaben 2027.
Tsohon gwamnan jihar Anambra ya ce yiwuwar tsayawa takara a zaben 2031 ba ta da yawa, saboda tsarin karba-karba na shugabancin kasa tsakanin Arewa da Kudu da ake bi a siyasar Najeriya.

Kara karanta wannan
Kurunƙus: Tinubu ya mika fam ga APC, ya zabi wanda zai masa mataimaki a zaben 2027

Source: Facebook
Tribune Nigeria ta ruwaito cewa Obi ya bayyana haka ne yayin wata hira da fitaccen dan jarida, Rufai Oseni, inda ya yi bayani kan makomarsa ta siyasa bayan zaben 2027.
Peter Obi ya fara hango bayan zaben 2027
Da aka tambaye shi ko zai sake neman takarar shugaban kasa idan bai yi nasara a 2027 ba, Obi ya ce matsayarsa za ta dogara ne da sakamakon zaben da kuma yadda za a tsara kujerun mulki kafin zaben 2031.
Ya ce:
"A gare ni, komai zai dogara da abin da zai faru a zabe na gaba. Ba na son in yi magana sosai saboda kada mutane su dauka ina nufin wasu ne."
Obi ya tuna tambayar wani dalibi
Peter Obi ya ce wani dalibin makarantar sakandare ya taba tambayarsa ko zai sake tsayawa takarar shugaban kasa bayan zaben 2027.
Ya ce ya amsa masa da cewa:
"Na ce masa idan ban tsaya takara yanzu ba, damar neman mulki za ta jima ba ta sake zuwa ba, idan aka bi tsarin karba-karba, mulki zai koma Arewa."
Obi ya bayyana cewa idan shugaban kasa daga Arewa ya hau mulki a 2031, lokacin da damar za ta sake komawa Kudu zai kai shekaru 78.
Mw zai sa Obi ya hakura da takara
A cewarsa:
"Idan mulki ya koma Arewa a 2031, lokacin da zai sake dawowa Kudu zan kai shekara 78, kuma ban ga zan ci gaba da wannan fafutuka a wannan shekarun ba."

Source: Facebook
Sai dai tsohon gwamnan ya ce idan har mulki ya ci gaba da kasancewa a Kudu a 2031, akwai yiwuwar ya sake yin tunanin tsayawa takara, kamar yadda Leadership ta kawo.
"Idan har mulki ya ci gaba da kasancewa a Kudu a zabe na gaba, watakila. Amma yiwuwar hakan ba ta da yawa. Ba zan iya tabbatar da komai ba sai bayan sakamakon zaben 2027."
- Peter Obi.
Peter Obi ya yi hasashen mutuwa kafin 2027
Kun ji cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi , ya ce akwai yiwuwar ba zai kai lokacin zaben 2027 mai zuwa ba.
Peter Obi ya bayyana cewa wataƙila ba zai kasance a raye ba balle ya fafata a zaben na shekarar 2027, yana mai zargin gwamnatin trayya da muzgunawa yan adawa.
Peter Obi ya kuma yi zargin cewa gwamnati ta taso 'yan adawa a gaba inda ya bada labarin wani abu da ya taba faruwa da shi.
Asali: Legit.ng
