Baban Chinedu Ya Yabi Nagartar Pantami amma ya Fadi Wurin Za a Nakasa Shi a Siyasa
- Yusuf Haruna ya tofa albarkacin bakinsa game da shigar malaman addini cikin harkokin siyasa a Najeriya
- Baban Chinedu kamar yadda aka fi sanin sa ya yi wa Sheikh Sani Jingir uzurin maganganun da yake yawan yi
- Tsohon ‘dan wasan kwaikwayon ya ce ana yawan kuka da Isa Ali Pantami wajen rashin iya mu’amala da mutane
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Katsina - Yusuf Haruna wanda kowa ya fi sani da Baban Chinedu ya tabo zancen Isa Ali Ibrahim Pantami da yake neman takara.
Malamin addinin ya fahimci abin da ya sa Sheikh Sani Jingir yake zakewa wajen tallata Bola Tinubu.

Source: Facebook
Tsokaci game da shigar malamai cikin siyasa
Tashar DCL Hausa ta yi hira da Yusuf Haruna a shirin siyasar zamani a matsayinsa na mai da’awar yada addinin Musulunci a Najeriya.
A fashin bakin da ya yi game da shigar malamai siyasa, ya yi tsokacin da ya ce ya yi ne tsakani da Allah SWT saboda an tambaye shi.
Yusuf Haruna ya fara da Sani Yahaya Jingir, wanda ya ce kaf Najeriya babu malamin Musulunci da ya sha wahala da kiristoci irin shi.
Uzurin da Baban Chinedu ya yi wa Sani Jingir
Ya ce sai da kiristoci suka yi yunkurin hana Sheikh Sani Yahaya Jingir yin sallah, bayan hallaka mutanen shi da-dama da aka yi.
Saboda wannan adawa a Jos ne ya ce Jingir ya dauki tallar tikitin Muslim-Muslim, amma duk da haka ya hararo kuskuren malamin.
Duk da ya yi masa uzuri, amma Baban Chinedu ya ce shehin bai la’akari da cewa yawon maganarsa ta wuce garin Jos, ana jin sa ko ina.
Baban Chinedu: 'Pantami ya cancanta amma bai da mu'amala'
A Gombe kuwa, Baban Chinedu ya nuna Isa Ali Pantami yana da damar neman takara, amma ya zarge shi da rashin iya hulda mutane.
Idan ana zancen ilmin zamani da yin kokarin lokacin da ya rike hukumar NITDA da minista a gwamnati, ya ce Isa Pantami ya yi fice.
Wani wuri da ya ga na raunin sa shi ne rashin taimakon ‘yan siyasa da yake ofis, ya ce za a rankwala shi da kasa tun wajen neman tikiti.
Ai bai da mu’amala. Gaba daya malam bai da mu’amala.
- Baban Chinedu
Da aka zo da kan batun nagarta, tsohon ‘dan wasan kwaikwayon ya yarda Pantami yana da nagartar rike har Najeriya, ya kuma rantse da Allah.
Baban Chinedu ya ce:
WalLahi yana da nagarta. Amma fa mu’amala a cikin 100%, bai fi 10% ya dauka ba. Ba ma da ‘yan siyasar ba, mu’amala ma da mutane shi bai iya ba.

Source: Facebook
Shawarar da aka ba Sheikh Pantami
Da ‘dan jaridar ya tambaya ko sauran malamai ba su ba shi shawara ya gyara, sai ya ce ba dole ba ne ya dauki shawarar ko an ba shi.
Baban Chinedu ya ce tunda ya shiga siyasa, ko da haka halin malamin addinin yake, ya kamata ya canza da nufin samun karbuwa.
“Malam bai da mu’amala, tsakani da Allah ba zan boye maka ba.”
Duk da shi ba ‘dan siyasa ba ne, Baban Chinedu ya ce ko da zaben tsaida gwani aka shiga, ba dole ba ne Isa Pantami ya samu nasara ba.
A cewarsa, idan shehin malamin ya yi sake, har a unguwarsu ta Pantami sai an doke shi duk da kasancewarsa mutumin kirki mai amana.
Baban Chinedu ya ce ya fadi wannan ne saboda ya yi hulda da shi kuma haka sauran wadanda suka yi alaka da Sheikh Pantami suke fada.
Pantami ya ziyarci coci a Gombe
Wannan rahoto ya dauko maku hudubar da Isa Ali Pantami ya yi a cocin ECWA a Gombe har da jawo ayoyin Bible da yake yi wa kiristoci jaje.
An ji yadda ta kaya tsakanin Isa Ali Pantami da kiristoci da shehin ya ziyarci coci a garin Gombe a sakamakon wata gobara da ta yi masu barna.
'Dan takaran gwamnan ya ce ba kamfe ya kawo shi ba illa ya yi masu jajen abin da ya faru da su.
Asali: Legit.ng


