Wike Ya Tsage Gaskiya kan Yiwuwar PDP Ta Iya Lashe Zaben Shugaban Kasa a 227

Wike Ya Tsage Gaskiya kan Yiwuwar PDP Ta Iya Lashe Zaben Shugaban Kasa a 227

  • Ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike ya ce PDP ba za ta iya lashe zaben shugaban kasa ba sai ta gyara rikicin cikin gida
  • Wike ya bayyana cewa wajibi ne jam'iyyar ta gyara tsarinta na cikin gida tun daga matakin mazabu har zuwa kasa kafin zaben 2027
  • Ministan ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne gina jam'iyya daga matakin kasa, tare da samun nasarori a jihohi kafin a fara tunanin karbe mulkin kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa zai yi wahala jam'iyyar PDP ta sake lashe zaben shugaban kasa a 2027 a halin da take ciki.

Wike ya bayyana cewa babu ta yadda PDP za ta iya lashe zabe matukar ba ta fara gyara tsarinta na cikin gida da warware rikice-rikicen da ke addabarta ba.

Kara karanta wannan

"Ba zan amince ba"; Wike ya gano dalilin rashin farin jininsa a wajen ma'aikata

Nyesom Wike.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike Hoto: Nyesom Wike
Source: Facebook

Wike ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai ranar Alhamis, 9 ga watan Yulin 2026, kamar yadda jaridar Punch ta rahoto.

Tsohon gwamnana na jihar Ribas ya ce babu wata jam'iyyar siyasa da za ta iya cin zaben shugaban kasa idan ba ta fara gina kanta daga tushe ba.

PDP na bukatar sake gina kanta

Wike ya amince cewa PDP na fuskantar matsaloli masu yawa, yana mai cewa sake mayar da jam'iyyar kan hanyar samun nasara a zaben shugaban kasa ba abu ne mai sauki ba.

Ya ce:

"Na fada cewa PDP tana da matsala. Idan kana da irin wannan matsalar, ba abu ne mai sauki ka dawo ka lashe zaben shugaban kasa ba.
"Ba ma batun zaben shugaban kasa kadai. Har gudanar da zaben mazabu ma yana da wahala."

Mafitar da Wike ya hango ga PDP

Ministan ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne gina jam'iyya daga matakin kasa, tare da samun nasarori a jihohi kafin a fara tunanin karbe mulkin kasa.

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta yi wa sojoji ƙarin lbashi mai gwaɓi don inganta walwalarsu a Najeriya

Ya ce:

"Abin da ya fi muhimmanci shi ne ku gina jam'iyya, ku nuna abin da za ku iya yi a matakin jiha, ku tattara kuri'un da za ku iya samu, sannan ku hada karfi ku shirya."

Wike ya ce samun nasara a zaben shugaban kasa na bukatar tsari mai karfi da kuma shiri na dogon lokaci, cewar rahoton Vanguard .

Jam'iyyar adawa.
Tutar jam'iyyar adawa a Najeriya, PDP Hoto: @OfficialPDPNigeria
Source: Twitter

Shin Wike na yiwa APC aiki?

Ministan na Abuja ya kuma yi martani kan zarge-zargen da aka taba yi masa cewa yana yi wa jam'iyyar APC aiki.

Ya ce:

"Ba ni ne aka rika cewa wakilin APC ba? Ina masu wannan zargin yanzu? Har yanzu ina nan, ban taba boye matsayina ba. Na dade ina fadawa jam'iyyarmu cewa mu gyara gidanmu."

Saƙon Wike ga 'yan takarar PDP

A wani labarin, kun ji cewa Ministan Abuja, Nyesom Wike , ya buƙaci mambobin jam'iyyar PDP da su shiryawa gagarumin yaƙin siyasa gabanin babban zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Akpabio ya yi hasashen abin da 'yan adawa za su ce idan Tinubu ya ci zaben 2027

Wike ya bayyana cewa ba a taɓa bayar da mulki haka kawai, sai dai ana samunsa ne ta hanyar fafutuka, sadaukarwa, da kuma aiki tuƙuru.

Ya shaida wa magoya bayan PDP cewa siyasar adawa tana buƙatar juriya, tsari, da kuma ƙuduri, inda ya yi gargaɗin cewa jam'iyyarNba za ta koma kan mulki ta hanyar takama ko tunani kawai ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262