2027: Ana Zargin Goyon Bayan Sheikh Pantami Ya Jefa Kamfanin Gombawa Motors a Matsala

2027: Ana Zargin Goyon Bayan Sheikh Pantami Ya Jefa Kamfanin Gombawa Motors a Matsala

  • Mahukunta sun umarci kamfanin sufuri na Gombawa Motors ya fice daga tshar mota ta Ibrahim Hassan Dankwambo Mega Park cikin sa’o’i 24
  • Matakin ya zo ne kwanaki biyu bayan kamfanin ya bayyana goyon bayansa ga dan takarar gwamnan PDP, Farfesa Isa Ali Pantami
  • Mahukuntan Mega Park sun ce korar ta samo asali ne daga zargin karya ƙa’idojin aiki da koke-koken masu sufuri, ba saboda siyasa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gombe, Nigeria - Gwamnatin Jihar Gombe ta kori kamfanin sufurin motoci na Gombawa Motors daga tashar Ibrahim Hassan Dankwambo Mega Park.

Matakin na zuwa ne awanni 24 bayan kamfanin ya fito fili ya bayyana goyon bayansa ga ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, Farfesa Isa Ali Pantami.

Gombawa.
Motar sufuri ta kamfanin Gombawa Motors da ke jihar Gombe Hoto: Aliyu Usman
Source: Facebook

An ba kamfanin wa’adin sa’o’i 24

Kara karanta wannan

Tallar kosai da karago: 'Yan Najeriya sun dura kan matar Tinubu bayan kalamanta

Jaridar Aminiya ta ruwaito korarar hakan na kunshe ne a wata sanarwa mai ɗauke da kwanan watan 25 ga Yunin 2026 kuma shugaban Principal Facilities Management Limited ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta umarci kamfanin Gombawa Motors da ya fice daga harabar tashar motoci ta Mega Park cikin sa’o’i 24, lamarin da wasu suka fara dangantawa da siyasa.

Matakin ya fito ne daga kamfanin Principal Facilities Management Limited wanda ke kula da tashar Mega Park, mallakin Gwamnatin Jihar Gombe.

Dalilin korar kamfanin Gombawa motors

A cewar sanarwar, mahukuntan tashar sun yanke hukuncin ne bisa zargin kamfanin da karya ƙa’idojin gudanar da ayyuka a bayan samun koke-koke daga sauran masu harkar sufuri.

An kuma aika kwafin umarnin zuwa Kamfanin Kula da Hanyoyi da Sauran Ababen More Rayuwa na Jihar Gombe (GROCOL), Rundunar ’Yan Sanda, Hukumar DSS da Hukumar NSCDC.

Sai dai takardar ba ta ambaci cewa goyon bayan da kamfanin ya nuna wa Pantami ne ya jawo daukar wannan mataki a kansa ba.

Mahukuntan Mega Park sun nace cewa an ɗauki matakin ne saboda zargin karya dokokin aiki da kuma koke-koken masu ruwa da tsaki, ba saboda ra’ayin siyasa ba.

Kara karanta wannan

Minista ya rutsa shugaban jami'a kan zargin nada hadimai 24 a ofishinsa

Kamfanin Gombawa Motors ya yi magana

A nasa ɓangaren, shugaban Gombawa Motors, Alhaji Ibrahim Mustapha, ya ce ƙungiyar ta amince da mara wa Farfesa Isa Ali Pantami baya, yana mai cewa sama da mambobi 4,000 ne suka goyi bayan wannan matsaya.

A rahoton Leadership, Mustapha ya kuma bayyana cewa tun bayan fara amfani da Mega Park, an sha sauya wa kamfanin wuraren aiki, lamarin da ya jawo musu babbar asarar kuɗi.

Pantami.
Dan takarar gwamnan jihar Gombe na jam'iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami Hoto: Professor Isa Ali Pantami
Source: Facebook

Ya ce sun kashe fiye da Naira miliyan 10 wajen gina tantuna, ofisoshi da sauran kayayyakin aiki a wani wuri da aka ware musu kafin daga bisani aka sake umartar su su koma wani wuri.

Pantami ya karbi shaidar takara a PDP

A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyar adawa ta PDP ta mika wa Farfesa Isa Ali Pantami takardar shaidar zama ɗan takarar gwamnan Gombe a zaben 2027.

Pantami ya karbi takardar shaidar ne ranar a taron Kwamitin Zartarwa na Kasa (NEC) na jam’iyyar a hedkwatar PDP da ke birnin Abuja.

Bayanai sun nuna cewa shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga sassan kasar nan daban-daban sun halarci taron NEC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262