'Dalilin da Ya Sa Shugaba Tinubu Zai Lallasa 'Yan Adawa a Zaben 2027'

'Dalilin da Ya Sa Shugaba Tinubu Zai Lallasa 'Yan Adawa a Zaben 2027'

  • Tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Kalu, ya ce Shugaba Bola Tinubu ba shi da wata babbar barazana daga 'yan adawa kafin zaɓen 2027
  • Sanata Kalu ya ce rashin haɗin kai tsakanin jam'iyyun adawa ya raunana ƙarfinsu wajen fuskantar APC
  • Sanatan ya kuma bayyana cewa aikin gwamnatin Tinubu zai sa al'ummar Arewacin Najeriya su mara masa baya a zaɓen 2027

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Kalu, ya yi magana kan tazarcen Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

Sanata Kalu ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba shi da wata babbar hamayya a gabansa kafin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Kalu ya hango nasarar Tinubu a zaben 2027
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: Bayo Onanuga
Source: Facebook

Kalu, mai wakiltar mazabar Abia ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya faɗi haka ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels TV da aka gabatar ranar Laraba, 5 ga watan Agustan 2026.

Kara karanta wannan

Bayani kan ƙarin albashi da Tinubu ya yi wa ƙanana da manyan sojojin Najeriya

Ya ce jam'iyyun adawa sun yi rauni matuƙa saboda sun gaza haɗuwa a ƙarƙashin tsari guda da kuma tsayar da ɗan takara ɗaya.

Kalu ya ce 'yan adawa sun yi rauni

A cewar Kalu, Shugaba Tinubu ba shi da wani babban abokin hamayya saboda rashin haɗin kai da ke tsakanin jam'iyyun adawa.

"Ba shi da wata hamayya. 'Yan adawa sun yi rauni sosai. Idan ka duba yadda muka gudanar da zaɓen fidda gwani, yawan mambobinmu da kuma abubuwan da Tinubu ya yi a faɗin Najeriya."
"Musamman sababbin hanyoyin da aka gina, za ka fahimci hakan. Da sun haɗa kai, da hakan zai sa mu fara shiga damuwa. Amma yanzu ba su haɗu ba." In ji shi

Ya ce Tinubu bai tallata ayyuka ba

Sanatan ya amince cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta yi nasarar isar da saƙon nasarorin da ta samu ga 'yan Najeriya yadda ya kamata ba. Ya ce shugaban ƙasar bai mayar da hankali wajen tallata ayyukan gwamnatinsa ba.

Kara karanta wannan

Alkawarin da Shugaba Tinubu ya yi ga yan Najeriya game da addininsu

Kalu ya ƙara da cewa Tinubu yana da "maƙiya da dama" a cikin gwamnati da kuma wajen gwamnati waɗanda ke aiki domin kawo cikas ga tafiyar mulkinsa.

Kalu ya yabawa aikin Tinubu

Kalu ya bayyana cewa shugaban ƙasar ya yi aiki mai kyau har zuwa yanzu. A cewarsa, Tinubu ya kai kusan 65% na abin da ake tsammani daga gare shi, kuma nan da watan Satumba ko Oktoba zai iya kaiwa 70%.

Ya kuma yi hasashen cewa al'ummar Arewacin Najeriya za su mara wa Tinubu baya idan lokacin zaɓe ya yi, saboda abin da ya bayyana a matsayin kyakkyawan aikin gwamnatinsa.

Kalu ya yabawa Shugaba Tinubu
Sanata Uzor Orji Kalu zaune a cikin ofis Hoto: Sen Uzor Orji Kalu
Source: Facebook

Rikice-rikicen adawa kafin zaɓen 2027

Kalaman Kalu na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da samun sauye-sauyen siyasa tsakanin jam'iyyun adawa gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

A shekarar 2025, yunƙurin kafa ƙawancen siyasa a ƙarƙashin jam'iyyar African Democratic Congress (ADC) ya haɗa fitattun 'yan siyasa da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

Sai dai rashin jituwa kan tsarin tafiyar da ƙawancen da kuma shugabancinsa ya haifar da sabon rabuwar kai a tsakanin 'yan adawar. Hakan ya sa Peter Obi da Rabiu Kwankwaso suka fice daga jam'iyyar ADC..

Kara karanta wannan

Bayan shan suka Gwamna Abba ya kare matakin ba 'yan APC filaye sama da 1500

Uba Sani ya yi wa Tinubu alkawari

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya nuna goyon bayansa ga tazarcen Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

Uba Sani ya bauyana cewa bai shakkar cewa Shugaba Tinubu zai samu kaso 95 na kuri'un mutanen Kaduna a zaben 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng