Ran Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Baci kan Surutu Babu Aiki, Ya Kawo Mafita
- Shugaban kungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kira kan matsalolin tsaro
- Gwamna Inuwa Yahaya ya yi kiran ne a ranar Litinin yayin da yake gabatar da saƙon fatan alheri a taron Majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa
- Taron ya samu halartar gwamnoni, sarakunan gargajiya, shugabannin hukumomin tsaro da wakilan gwamnatin tarayya domin tattauna batun tsaro
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Jigawa — Shugaban kungiyar gwamnonin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kira da a ɗauki matakan gaggawa kuma masu ƙarfi domin magance matsalolin tsaro, talauci da rashin ci gaba da ke ƙara ta’azzara a Arewacin Najeriya.
Ya yi magana yana mai bayyana cewa lokacin yawan taruka da fitar da shawarwari ba tare da aiwatar da su ba ya kamata ya zo ƙarshe.

Source: Facebook
Mai magana da yawun Inuwa Yahaya, Isma'ila Uba Misilli ya wallafa a Facebook cewa gwamnan ya yi maganar ne da yake jawabi a taron majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa a Dutse, jihar Jigawa.
Kira ga shugabannin Arewa
Inuwa Yahaya ya buƙaci 'yan siyasa, sarakuna, hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su wuce matakin magana kawai su rungumi mafita ta zahiri da za ta iya dawo da zaman lafiya, kwanciyar hankali da bunƙasar yankin.
Ya bayyana halin tsaro a yankin a matsayin abin damuwa ƙwarai, yana mai cewa ’yan bindiga, rikicin makiyaya da manoma sun cigaba da lalata al’ummomi, kawo cikas ga tattalin arziki da raunana haɗin kan jama’a.
“Idan ba tsaro, babu haɗin kai. Idan ba tsaro da haɗin kai ba, ba za a samu cigaba ba,”
In ji shi.
Alakar talauci da matsalar tsaro
Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa matsalar tsaro a Arewa ba ta samo asali daga aikata laifffuuka kaɗai ba, tana da alaƙa da shekaru masu yawa na rashin kula da harkokin zamantakewa da tattalin arziki.
A cewarsa, kimanin mutane miliyan 86 a Arewacin Najeriya na fama da talauci mai fuskoki da dama, yayin da yankin ke ɗauke da mafi yawan yara marasa zuwa makaranta a ƙasar.
Ya yi gargaɗin cewa yaɗuwar talauci, rashin aikin yi da ƙarancin damar samun ilimi sun samar wa ƙungiyoyin masu laifi da masu tsattsauran ra’ayi damar ɗaukar matasa masu rauni zuwa cikinsu.

Source: Facebook
Kiran yin gyare-gyare a Arewa
Domin sauya wannan hali, Inuwa Yahaya ya ba da shawarar aiwatar da manyan gyare-gyare da suka haɗa da kafa ’yan sandan jihohi, ƙara zuba jari a ilimi da koyar da sana’o’i, ƙarfafa matasa, farfaɗo da harkar noma.
Ya kuma buƙaci shugabannin Arewa su nuna ƙwazo wajen aiwatar da shawarwarin da ake cimmawa zuwa aiki a zahiri:
“Mun gaji da tarukan da ba sa haifar da sakamako. Mun gaji da sanarwar bayan taro da ba a aiwatarwa. Mun gaji da alkawuran da ba a cikawa,”
In ji shi.
Gwamnan Gombe ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnatin da al’ummar Jihar Katsina kan rasuwar Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya.
Vanguard ta wallafa cewa Inuwa Yahaya ya jaddada muhimmiyar rawar da sarakunan gargajiya ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.
Jihar Katsina ta dauki matakan tsaro
A wani labarin, mun kawo muku cewa Gwamnatin jihar Katsina ta dauki sababbin matakan tsaro domin yaki da 'yan ta'adda masu garkuwa da mutane.
Gwamna Dikko Radda ya sanar da cewa an hana sana'ar cajin waya, acaba, POS da sayar da fetur a cikin jarakuna a wasu kananan hukumomi.
Yayin da ya ke gargadi ga jama'a, Dikko Radda ya bayyana cewa ba za a sassauta wa duk wanda ya karya dokokin da aka sanya a jihar ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


