"Ko Ganduje ba zai Ce Shi ba Yarona ba ne": Kwankwaso Ya Yi Martani ga Abba

"Ko Ganduje ba zai Ce Shi ba Yarona ba ne": Kwankwaso Ya Yi Martani ga Abba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa. Jihar Kano – Jagoran ƙungiyar Kwankwasiyya kuma jigo a jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake mayar da martani ga Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, kan takaddamar da ke tsakaninsu ta siyasa.

Kwankwaso ya bayyana cewa babu wani abin mamaki idan ya kira wasu mutane “yaransa” a siyasa, domin a cewarsa ya taimaka wajen ɗaga su zuwa manyan muƙamai.

Kara karanta wannan

NDC: An gano wanda Kwankwaso ke so ya tsayar ya fafata da Abba a Kano

Kwankwaso ya yi m artani ga Abba
Gwamna Abba Kabir Yusuf tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso
Source: Twitter

Tsohon gwamnan na Kano ya yi wannan bayani ne yayin da yake jawabi ga magoya bayansa a gidansa da ke Miller Road a Kano ranar Laraba, 27 ga watan Mayu, 2026 kamar yadda hadiminsa, Hon Saifullahi Hassan ya wallafa a Facebook.

Kwankwaso ya ce Abba yaronsa ne

Da yake magana ga magoya bayansa, Kwankwaso ya ce wasu mutane suna nuna rashin ladabi idan suka ƙi amincewa cewa sun taɓa zama yaransa a siyasa.

Rabiu Musa Kwanwkas ya ce Abba yaronsa ne
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso tare da magoya bayansa a Kano Hoto: Hon. Saifullahi Hassan
Source: Twitter

Ya ce:

“Na ji wasu suna cewa ba sa son a kira su yara. Idan ba rashin kunya ba, ta yaya Mai Gidan Ruwa ko Aminu Goro za su ce ba yarana ba ne a siyasa?"

Kwankwaso ya ƙara da cewa Ganduje, wanda ya yi wa’adin shekaru takwas a matsayin mataimakinsa kafin daga baya ya zama gwamna, yana cikin mutanen da suka amfana da tafiyarsa ta siyasa.

"Ta yaya ma Ganduje zai musanta cewa ya taɓa zama yarona?”

Kara karanta wannan

Tsohon hadimin shugaban APC na kasa, Mustapha Dawaki ya bi tafiyar Kwankwaso a Kano

Dangantaka na tsami tsakanin Abba da Kwankwaso

Kalaman Kwankwaso na zuwa ne bayan Abba Gida Gida ya yi shi ne karo na farko da ya fito fili yana sukar Kwankwaso tun bayan rabuwar da aka samu tsakaninsu a farkon wannan shekarar.

Gwamnan ya ce yawan kalaman da Kwankwaso ke yi a kansa sun yi yawa, amma shirun da ya yi bai kamata a ɗauke shi a matsayin tsoro ba.

Haka kuma ya gargadi jagoran Kwankwasiyyar da ya mutunta kansa, in ba haka ba zai fito ya bayyana wasu abubuwa da ke ɓoye. Tun bayan da Gwamna Yusuf ya rabu da Kwankwaso, tsohon ubangidansa na siyasa ya riƙa zarginsa da cin amanar tafiyar Kwankwasiyya.

Kwankwaso ya ce Abba Kabir Yusuf ya samu nasarar lashe zaɓe ne a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP, amma daga baya ya koma jam’iyyar APC mai mulki.

Takaddamar da ke tsakanin jagororin biyu na ci gaba da jan hankalin al’ummar Kano, yayin da masu bibiyar siyasa ke sa ido kan yadda rikicin zai kaya gabanin zaɓukan 2027.

Kara karanta wannan

Takarar 2027: Yadda Abba Kabir Yusuf ya sasanta manyan 'yan APC a Kano

Tsohon mataimakin gwamna ya magantu kan Abba

A baya, mun kawo labarin cewa tsohon mataimakin gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya yi magana kan sabanin da ya shiga tsakaninsa da gwamna Abba Kabir Yusuf.

Tsohon mataimakin gwamnan ya soki manufar “Kano First” tare da cewa tsaro ya kara tabarbarewa a jihar Kano, inda ya bayyana cewa an dauko tsarin 'yan mulkin mallaka ne a jihar Kano.

Kwamred Aminu Abdulsalam, wanda ya yi murabus daga mukaminsa ya bayyana matsayarsa game da neman kujerar tsohon mai gidansa a jam'iyyar NDC yayin da ake fitar da 'yan takara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng