An Tsinci Gawar Malami a Yashe, an Ce Wasu ne Suka Daɓa Masa Wuka har Lahira

An Tsinci Gawar Malami a Yashe, an Ce Wasu ne Suka Daɓa Masa Wuka har Lahira

  • An gano gawar wani limamin cocin Katolika a Ajaokuta, bayan an daba masa wuka tare da yi masa munanan raunuka
  • Rundunar 'yan sandan Kogi ta ce jami'anta sun garzaya wurin da aka tsinci gawar, suka kai ta asibiti, inda likita ya tabbatar da rasuwarsa
  • 'Yan sanda sun ce suna gudanar da bincike domin gano tare da cafke wadanda suka kashe limamin, kafin mika shari'ar zuwa sashen binciken manyan laifuka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ajaokuta, Kogi - An gano gawar wani limamin cocin Katolika, Fasto Samuel Opeyemi, a yankin Ajaokuta da ke Kogi bayan wasu mutane sun kashe shi.

Kafin rasuwarsa, marigayin yana gudanar da aikin limanci a cocin St. Mary's Catholic Church da ke garin Egbe, inda yake yi wa mabiya hidima.

An tsinci gawar fasto a Kogi
Taswirar jihar Kogi da aka kashe fasto. Hoto: Legit.
Source: Original

Rahotanni sun ce an daba wa Fasto Opeyemi wuka sau da dama, sannan aka tsinci gawarsa a gefen hanya a yankin Ajaokuta da ke Kogi, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

An kama dan shekara 20 da zargin ba 'yan bindiga makamai

Jami'ar hulda da jama'a ta rundunar 'yan sandan Kogi, ASP Afusat Salihu, ta tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa da ta fitar.

Ta bayyana cewa rundunar ta samu rahoton gano gawar wani namiji da ba a san ko wane ne ba a bakin titin Church Road da ke Ajaokuta.

Ta ce da isar jami'ai wurin, sun tarar mamacin na dauke da munanan raunukan sara da adda a kansa, sannan aka kai gawarsa asibitin ASCL.

Likitan da ya duba gawar ya tabbatar da rasuwarsa, daga bisani aka ajiye gawar a dakin ajiye gawa domin gudanar da binciken gawar.

Bayan tantancewa, an tabbatar cewa mamacin Fasto Samuel Opeyemi ne daga cocin St. Paul Parish da ke Ayetoro Gbede a karamar hukumar Ijumu, yayin da 'yan sanda ke ci gaba da bincike domin cafke wadanda suka aikata kisan.

Meta description (kasa da kalmomi 30):

Ƙarin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.