Atiku vs Amaechi: ADC Ta Sanar da Sakamakon Zaben Fitar da 'Dan Takarar Shugaban Kasa a Kano
- Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar na ci gaba da samun nasara a zaben fitar da gwanin jam'iyyar adawa ta ADC
- Shugaban kwamitin zaɓen, John Ayuba, ya ce Atiku ya samu nasara a Kano da ƙuri’u 155,595 yayin da Amaechi ya samu ƙuri’u 9,994
- Wannan na zuwa ne bayan Atiku ya samu nasara a jihohi biyar, lamarin da ya sa ya shiga gaban sauran masu neman takarar shugaban kasa a inuwar ADC
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya lashe zaɓen fitar da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a Jihar Kano.
Shugaban kwamitin zaɓen, John Ayuba, ya bayyana cewa an gudanar da zaɓen a dukkan ƙananan hukumomi 44 da kuma gundumomi 484 na jihar.

Source: Facebook
Yadda sakamakon ya kasance a Kano
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa bisa ga sakamakon da aka tattara daga kananan hukumomin Kano, Atiku ya samu ƙuri’u 155,595.
Masanin tattalin arziki, Mohammed Hayatu-Deen ya zo na biyu da ƙuri’u 15,914, yayin da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya samu ƙuri’u 9,994.
Dr Ayuba ya ce za a tura sakamakon zuwa cibiyar haɗa sakamakon zaɓe ta jam’iyyar a Abuja domin tantancewa da kuma ayyana ɗan takarar shugaban ƙasa a hukumance.
Atiku ya shiga gaba a zaben ADC
Ya kuma buƙaci mambobin jam’iyyar su ci gaba da haɗa kai domin tabbatar da ADC ta samar da shugaban Najeriya na gaba.
Wannan na zuwa ne bayan Atiku ya samu nasara a jihohi biyar, lamarin da ya sa ya shiga gaban sauran masu neman takarar shugaban kasa a inuwar ADC da mafi rinjayen kuri'u.
Daga cikin jihohin da tsohon mataimakin shugaban kasar ya lashe akwai Sakkwato, Gombe, Abia, Zamfara da Ebonyi.
Shin ADC ta tsaida dan takarar gwamna?
A daya ɓangaren kuma, jam’iyyar ta dakatar da sanar da sakamakon zaɓen fitar da gwani na takarar gwamnan jihar Kano har sai shugabancin jam’iyyar ADC na ƙasa ya yanke hukunci.
Ana fafatawar ne tsakanin Ibrahim Ali Amin Little da Ibrahim Khalil, yayin da jam’iyyar ke nazarin yiwuwar amfani da tsarin maslaha domin zaɓen ɗan takararta.
Jam'iyyar ADC ta dakatar da sanar da sakamakon ne saboda takaddamar da ta biyo baya, inda a yanzu uwar jam'iyya ta kasa za ta yanke hukuncin karshe.
A wani labarin, kun ji cewa
Asali: Legit.ng

