Atiku Ya Lallasa Yan Takara 2, Ya Samu Nasara a Zaben Fitar da Gwanin ADC a Sakkwato
- Sakamakon fitar da gwanin jam'iyyar ADC na takarar shugaban kasa da aka gudanar yau Litinin ya fara fitowa daga jihohin Najeriya
- Atiku Abubakar ya samu ƙuri’u 68,823 inda ya kayar da sauran ‘yan takarar da suka fafata, Rotima Amaechi da Mohammed Hayatu-Deen a Sokoto
- Daga cikin manyan kusoshin da suka halarci wurin tattara sakamakon akwai tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Sokoto, Nigeria - Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya samu rinjaye a zaben fitar da 'dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC da aka gudanar a jihar Sakkwato.
Idan baku manta ba, jam'iyyar adawa ta ADC ta gudanar da zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa a yau Litinin, 25 ga watan Mayu, 2026 a fadin jihohin Najeriya.

Source: Facebook
ADC ta sanar da sakamako a Sakkwato
Daily Trust ta ruwaito cewa a sakamakon da aka bayyana a jihar Sakkwato, ya nuna cewa Atiku ya kayar da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da masanin tattalin arziki, Mohammed Hayatu-Deen.
Babban jami’in tattara sakamakon zaɓen a jihar Sakkwato, Aminu Abubakar, ne ya sanar da sakamakon a ranar Litinin, yana mai cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana.
Ya ce Atiku Abubakar ya samu ƙuri’u 68,823 inda ya kayar da sauran ‘yan takarar da suka fafata a zaɓen.
Atiku ya kayar da Amaechi a Sakkwato
Bisa ga sakamakon da aka bayyana, tsohon gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, ya samu ƙuri’u 292, yayin da Muhammad Hayatuddeen ya samu ƙuri’u 319.
Malamin jami’ar ya ce jimillar ƙuri’u 69,434 aka kaɗa a zaɓen fitar daa gwanin jam'iyyar hadaka ta ADC, kamat yadda Leadership ta kawo.
“Saboda haka ina ayyana Alhaji Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa wanda ya samu mafi yawan ƙuri’u a jihar Sokoto,” in ji shi.

Kara karanta wannan
"Ba dan koyo ba"; Atiku ya gano dan takarar da ya cancanci tutar ADC don karawa da Tinubu 2027
An sanar da sakamakon ne a gaban jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), jami’an tsaro da shugabannin jam’iyya.
Manyan jiga-jigan ADC sun halarci wurin
Daga cikin manyan kusoshin da suka halarci wurin tattara sakamakon akwai tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, da ɗan takarar gwamna na ADC a jihar, Mannir Dan Iya.

Source: Facebook
Haka zalika, ɗan takarar Sanatan Sokoto ta Kudu, Faruk Malami Yabo, da shugaban jam’iyyar ADC na jihar, Abdullahi Maigwandu da sauransu sun halarci wurin.
Tun da farko ADC a jihar Sakkwato ta ayyana Atiku a matsayin ɗan takara guda tilo da take goyon baya kafin gudanar da zaɓen fitar da gwanin.
Atiku ya yi magana kan takarar ADC
A wani rahoton, kun ji cewa Atiku Abubakar ya bayyana cewa dole ne jam'iyyar ADC ta tsayar da ɗan takara da ya cancanta da kuma gogewa, wanda zai iya warware matsalolin Najeriya.
Atiku ya ce zaɓin da ke gaban wakilan ADC ya wuce batun siyasa kawai, inda ya bayyana shi a matsayin wani babban nauyi na tarihi.
A cewar tsohon mataimakin shugaban kasar, an kafa ADC ne a kan ginshiƙai na gaskiya, riƙon amana, haɗa kai, da kuma sabunta tsarin demokraɗiyya.
Asali: Legit.ng
