Pantami Ya Fice daga Jam'iyyar APC, Ya Samu Tikitin Takarar Gwamna a Jihar Gombe

Pantami Ya Fice daga Jam'iyyar APC, Ya Samu Tikitin Takarar Gwamna a Jihar Gombe

  • Farfesa Isa Ali Pantami ya sauya sheka daga APC mai mulki zuwa jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Gombe bayan rasa rikitin takara
  • Tsohon ministan na sadarwa ya kuma samu tikitin takarar gwamnan jihar Gombe a zaben 2027 karkashin inuwar jam'iyyar PDP
  • Masu zuwa da tsakin PDP a Gombe ne suka tabbatar da Pantami a matsayin dan takarar gwamna a wani taro da aka gudanar yau Talata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gombe, Nigeria - Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya sauya sheka daga jam'iyyar APC zuwa PDP a jihar Gombe.

Bayan saiya shekarsa, Pantami ya kuma ya lashe tikitin takarar gwamnan jihar Gombe a inuwar jam'iyyar PDP a zaben 2027 da ke tafe.

Pantami.
Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami a taron da PDP ta tsaida shi takara a jihar Gombe Hoto: Abba Sani Pantami
Source: Facebook

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa an ayyana Sheikh Pantami a matsayin dan takarar gwamnan PDP ne ta hanyara amincewa da baki a zaben fitar da gwanin da aka gudanar ranar Talata a Gombe.

Kara karanta wannan

Nnaji: Ministan da Tinubu ya kora saboda jabun takardu ya samu takarar gwamna a PDP

Mambobin jam'iyyar PDP ne suka amince da bai wa tsohon ministan takara ba tare fa hamayya ba a yau Talata, 26 ga watan Mayu, 2026.

Shugaban kwamitin zaɓe na Jam'iyyar PDP, Hon. Gregory Yenlong, ne ya bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen fitar da gwani, bayan da ya kasance ɗan takara guda ɗaya tilo da ya nemi takara

Da yake jawabi jim kaɗan bayan bayyana shi a matsayin 'dan takara, Pantami ya bayyana cewa ya fito neman kujerar gwamna ne domin ya bayar da tashi gudunmawar wajen yi wa al'ummar jihar hidima.

Ya yi alƙawarin cewa idan aka zaɓe shi a 2027, zai gudanar da mulki cikin gaskiya da adalci.

A yanzu Pantami zai fafata da Jamilu Gwamna, ɗan takarar gwamna na jam'iyyar APC a jihar Gombe.

Tun farko dai Pantami ya soki tsarin da ya bai wa Gwamna tikitin takarar APC ta hanyar maslaha.

Ya nemi a gudanar da zaɓen fitar da gwani kai tsaye, amma ya janye daga takarar kwana guda kafin zaɓen, yana zargin rashin gaskiya da adalci a tsarin.

Kara karanta wannan

2027: Mohammed Abacha ya sha kaye, PDP ta tsaida dan takarar gwamna a jihar Kano

‘Yan takarar PDP sun nuna adawa

Bayan kammala zaɓen fitar da gwani a APC, wasu ‘yan takarar gwamna huɗu na PDP sun nuna damuwa kan yunkurin shigar da Pantami cikin takarar gwamna ta PDP.

Sai dai duk da wannan adawa, shugabannin PDP a jihar Gombe sun zaɓi Pantami a matsayin wanda zai ɗaga tutar jam’iyyar a zaɓen gwamna na 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262