"Kamar Nadin Sarauta," Masani Ya Yi Kaca Kaca a Nasarar da Tinubu Ya Samu a APC

"Kamar Nadin Sarauta," Masani Ya Yi Kaca Kaca a Nasarar da Tinubu Ya Samu a APC

  • Masana sun fara tofa albarkacin bakinsu kan zaben fitar da dan takarar shugaban kasa da jam'iyyar APC ta gudanar
  • Shugaban Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara da gagarumin rinjaye, inda ya tika dan kasuwa, Stanley Osifo da kasa a zaben
  • Jide Ojo, wani mai sharhi kan harkokin yau da kullum ya ce zaben fidda gwanin APC ya yi kama da nadin sarauta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Masanin harkokin jama’a na yau da kullum, Jide Ojo, ya soki zaben fitar da gwanin jam'iyyar APC na shugaban kasa, wanda aka gudanar ranar Asabar da ta gabata.

Mista Ojo ya kwatanta zaben, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara,da 'nadin sarauta', yana mai cewa babu wata gwabzawa ta hakika da aka yi a zaɓen.

Osifor da Tinubu.
Dan kauswa, Stanley Osifo da shugaban kasa, Bola Ahmed Tonubu yana addu'a a masallaci Hoto: @aonanuga1956
Source: Facebook

Ojo ya bayyana hakan ne a shirin The Morning Brief na Channels TV ranar Litinin yayin da yake martani kan zaɓen fitar da gwani na APC da aka gudanar a mazaɓu 8,809 da ke jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

'Dan gwagwarmaya Sowore ya fito takarar shugaban kasa, zai kara da Tinubu a 2027

Masani ya soki zaben ftar da gwanin APC

A cewarsa, tun farko alamu sun nuna cewa an riga an tsara sakamakon zaɓen, yana mai cewa da jam’iyyar ta ɗauki lokaci sosai wajen shirya zaɓen, da an samu gasa mai ma’ana.

“Ina ganin cewa wannan zabe da aka yi tamkar naɗin sarauta ne kawai, dauka aka yi aka dora, an riga an taara komai tun farko.
"Wani mutum ya kashe Naira miliyan 100 sannan ya samu ƙuri’u 16,503 kacal, a jihohi 21 bai samu ko ƙuri’a ɗaya ba, a jiharsa ta Edo ya samu ƙuri’a ɗaya ne kawai,” in ji shi.

Ojo na magana ne kan ɗan kasuwa kuma tsohon mamban PDP, Stanley Osifo, wanda ya fafata da Shugaba Bola Tinubu bayan sayen fom ɗin takarar shugaban ƙasa na APC kan kudi Naira miliyan 100.

Tinubu ya lashe zaɓen da jimillar ƙuri’u miliyan 10.9, yayin da Osifo ya samu ƙuri’u 16,503, kamar yadda Leadership ta kawo.

Kara karanta wannan

'Ba za mu bar 'yan adawa ba,' Tinubu ya magantu kan zaben 2027

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a wurin taro Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Ojo ya yi sharhi kan takarar Osifor

Sai dai Ojo ya ce Osifo na da cikakken ‘yancin shiga takarar kuma ya kara da Shugaba Tinubu komai kankantar sakamakon da ya samu.

“Wasu na cewa ɗaukar nauyinsa aka yi, amma babu wata hujja da ta tabbatar da hakan. Abin da muka sani shi ne ɗan kasuwa ne, ya kashe Naira miliyan 100 nasa, kuma yau mutane na magana a kansa.
“Ya saka sunan iyalinsa a taswirar siyasar Najeriya idan ana maganar zaɓen 2027," in ji shi,.

Masanin ya ƙara da cewa shiga takarar da Osifo ya yi zai ci gaba da zama wani ɓangare na tattaunawar siyasar Najeriya yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

Shin Tinubu ya cancanci wa'adi na 2?

A wani labarin, kun ji cewa ministan lafiya, Muhammad Ali Pate ya yi bayanin abin da ya sa yake ganin Shugaba Bola Tinubu ya cancanci tazarce a zaben 2027.

Kara karanta wannan

"Ni ma na rame": Tinubu ya amince manufofinsa sun jefa ƴan Najeriya a wahala

Ministan ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya cancanci yan Najeriya su sake zaɓensa karo na biyu duba da nasarorin da gwamnatinsa ta samu a shekara uku.

Ali Pate ya ce daga cikin nasarorin gwamnatin Bola Tinubu har da samar da aikin yi ga matasa sama da 3,000 a Jihar Bauchi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262