Babbar Magana: An Bayyana Abin da Ke Kashe Mutane Fiye da 'Yan Bindiga a Najeriya

Babbar Magana: An Bayyana Abin da Ke Kashe Mutane Fiye da 'Yan Bindiga a Najeriya

  • MiDaraktan asibitin UNIMEDTH ya yi gargadin cewa jabun magunguna na zama babbar barazana ga lafiyar jama’a
  • Farfesa Michael Gbala ya bayyana cewa amfani fa jabun magunguna na iya zama hadari ga mutane ciye da illar yan bindiga
  • ya buƙaci masu ruwa da tsaki su inganta hanyoyin saye, rarrabawa da sa ido kan magunguna domin kare marasa lafiya daga amfani da jabun magunguna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ondo- Babban Daraktan Asibitin Koyarwa na Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta Ondo (UNIMEDTH), Farfesa Michael Gbala, ya nuna damuwa kan ƙara yaɗuwar jabun magunguna da marasa inganci a Najeriya

Ya fadi haka ne da yake magana yayin ziysrar da Babban Mai Ba da Shawara kan Zuba Jari a Fannin Magunguna da Kiwon Lafiya ga Gwamnatin Jihar Ondo, Dakta Samuel Oluwaoromipin Adekota, ya kai wa asibitin a ranar Laraba.

Kara karanta wannan

Abubuwan da ya dace a sani game da yarjejeniyar da aka yi tsakanin Musulmi da Kiristocin Najeriya

Michael Gbala
Babban Daraktan Asibitin Koyarwa na Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta Ondo (UNIMEDTH), Farfesa Michael Gbala tare da Dr. Samuel Oluwaoromipin Adekota Hoto: Unimed Teaching Hospital
Source: Facebook

Farfesa Gbala ya yi gargadin cewa jabun magunguna na iya yin sanadin mutuwar mutane fiye da ’yan bindiga, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Ya ce akwai buƙatar ɗaukar matakan gaggawa domin kare tsarin samarwa da rarraba magunguna daga shiga cikin matsala.

Illar da ke tattare da magungunan jabu

Bayan taron, shugaban UNIMEDTH ya jaddada illar magungunan da ba su da inganci da kuma jabun magunguna, yana mai bayyana su a matsayin barazanar ɓoye amma mai matuƙar haɗari ga lafiyar jama’a.

“Jabun magunguna na kashe mutane da sauri fiye da ’yan bindiga,” in ji shi, yana mai jaddada buƙatar tsaurara sa ido da tabbatar da inganci wajen saye da rarraba magunguna.

Abin da ya taba faruwa da Farfesa Gbala

Gbala ya tuna da wata matsala da ta taɓa faruwa da shi da ta ƙara nuna masa muhimmancin lamarin.

Ya bayyana cewa a wani lokaci ya fara shakkar sahihancin wani magani da ya saya wa ’yarsa duk da cewa ya biya kuɗi mai yawa.

Kara karanta wannan

Kasar Birtaniya ta aiko saƙo Najeriya bayan APC ta sha kaye a zaben gwamnan jihar Osun

A cewarsa, cibiyoyin kiwon lafiya ya kamata su ƙara mayar da hankali kan inda aka samo magungunan da ake bai wa marasa lafiya da kuma ingancinsu.

Ya ce sayen magani daga sanannen mai samar da magunguna ba lallai ne ya tabbatar da cewa maganin na gaske ne ba.

“Kasancewarsa daga hukumar samar da magunguna (DMA) ba ya tabbatar da cewa magani ne na gaske,” in ji Gbala.
Magunguna.
Wasu magunguna da aka kama bisa zargin na jabu ne Hoto: Picture Alliance
Source: Getty Images

Wane mataki ya kamata a dauka?

Babban Daraktan ya buƙaci masu ruwa da tsaki su inganta hanyoyin saye, rarrabawa da sa ido kan magunguna domin kare marasa lafiya daga amfani da jabun magunguna ko waɗanda ba su da inganci.

Ya kuma yi kira da a riƙa adana cikakkun bayanai kan umarnin sayen magunguna da kuma lokutan da masu samar da magunguna suka kasa cika buƙatun da aka gabatar musu.

Likita ya rasu bayan isa asibiti

Kun ji cewa wani kwararren likitan da ke aiki a Jihar Kano ya rasu bayan ya fadi jim kadan bayan ya isa Asibitin Arewa Surgery da ke Hotoro.

Lamarin ya faru ne bayan an bukaci marigayin, wanda aka bayyana sunansa da Dokta Ibrahim, ya mayengurbin wani likitan da ya kasa halartar aikinsa na yamma a asibitin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262