Babbar Kotu Ta Soke Tsarin INEC, Ta Sauya Lissafin Babban Zaben 2027 a Najeriya
- Babbar kotun tarayya ta soke wa'adin zaben fitar da gwani da na mika sunayen yan takara da hukumar INEC ta sanya wa jam'iyyun siyasa
- Mai shari'a Mohammed Umarya bayyana cewa wa'adin da INEC ta sanya sun saba wa tanade-tanaden dokar zabe ta 2026
- Sauran wadanda kotun ta soke sun hada da miƙa bayanan ‘yan takara, janye ko sauya ‘yan takara, fitar da jerin sunayen ƙarshe da kuma wa’adin dakatar da kamfe
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta soke Sabon Jadawalin Zaɓen 2027 da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fitar, lamarin da ya bai wa ‘yan siyasar da suka faɗi zaɓen fitar da gwani sabon fata.
Kotun ta ce wa’adin da INEC ta ɗora wa jam’iyyun siyasa domin gudanar da zaɓen fitar da gwani, miƙa sunayen ‘yan takara, maye gurbin wasu “ya saɓa da Dokar Zaɓe ta 2026."

Source: Getty Images
Mai shari’a Mohammed Umar na babbar kotun mai zama a Abuja ne ya yanke hukuncin a ranar Laraba, 20 ga watan Mayu, 2027, kamar yadda This Day ta ruwaito.
An shigar da ƙarar ne domin ƙalubalantar jadawalin da INEC ta tsara na zaɓen 2027, wanda aka ce an yi ne domin hana waɗanda suka faɗi zaɓen fitar da gwani komawa wata jam’iyya su sake neman takara.
Kwafin hukuncin kotun ya nuna cewa jam’iyyar Youth Party ce ta shigar da ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/517/2016, inda ta sanya INEC a matsayin wadda ake ƙara.
Kotu ta yi wa INEC gyara
Bayan sauraron ɓangarorin biyu, Mai shari’a Umar ya ce bisa sashe na 29(1) na Dokar Zaɓe ta 2026, jam’iyyun siyasa na da damar miƙa bayanan ‘yan takararsu har zuwa kwanaki 120 kafin zaɓe.
Saboda haka, ya ce INEC ba ta da ikon rage wannan wa’adi ta hanyar saka ƙarin takura a jadawalinta.
Haka kuma kotun ta ambaci sashe na 31 na dokar, wanda ya bai wa jam’iyyu damar janye ko sauya ɗan takara har zuwa kwanaki 90 kafin zaɓe.
Hukuncin da babbar kotun ta yanke
Daga ƙarshe, kotun ta soke duk wa’adin da INEC ta saka a sabon jadawalin zaɓen 2027 wanda ya saɓa da tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026.
Wadanda kotun ta soke sun haɗa da wa’adin gudanar da zaɓen fitar da gwani, miƙa bayanan ‘yan takara, janye ko sauya ‘yan takara, fitar da jerin sunayen ƙarshe da kuma wa’adin dakatar da yaƙin neman zaɓe.
Asali: Legit.ng

