"Shirun da Muka Yi ba Tsoro ba ne," Gwamna Abba Ya Tura Zazzafan Sako ga Kwankwaso
- Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargadi tsohon ubangidansa na siyasa, Rabiu Kwankwaso da ya ja girmansa
- Abba Gida-Gida ya bayyana cewa idan Kwankwaso ya ci gaba jifarsa da kalamai mara dadi, to zai fara maida martani
- Gwamnan ya ce kada a dauki shirun da ya yi a matsayin tsoro, yana mai gargadin cewa zai fara magana idan aka kai shi bango
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya fara gajiya da kalamai mara dadi da tsohon dan takarar shugaban kasa, Sanata Rabiu Kwankwaso ke jefo masa.
Gwamna Abba ya gargadi tsohon ubangidan nasa da cewa ya kamata ya rike girmansa, yana mai cewa shirun da yake yi ba tsoro ba ne.

Source: Facebook
Gwamna Abba ya aika sako ga Kwankwaso

Kara karanta wannan
"Dama sharrin shaidan ne": Abba ya kawo ƙarshen rikicin Rurum da Kawu Sumaila a Kano
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Abba Gida ya yi wannan furuci ne a wurin taron tabbatat da Sanata Kawu Sumaila a matsayin dan takarar sanatan Kano ta Kusu na APC a zaben 2027.
Gwamnan ya ce zaman lafiya a Kano shi ne abin da gwamnatin sa ta fi bai wa muhimmanci, amma idan aka ci gaba da matsa masa, zai fara maida martani.
Wannan ne karo na farko da aka ji Gwamna Abba ya yi raddi ga madugun Kwankwasiyya tun bayan rabuwar da suka yi a farkon wannan shekara ta 2026 da muke ciki.
Yadda Kwankwaso ke sukar Abba Kabir
Kwankwaso ya sha fitowa yana sukar gwamnan Kano, tare da kalaman da ke nuna gori kan taimakon da ya masa har ya samu nasara a zaben 2023.
Ko a baya-bayan nan, madugun Kwankwasiyya ya fito a wata hira da aka yi da shi, ya ce Abba Kabir ya yi babban kuskure da ya fice daga tafiyar Kwankwasiyya, in ji rahoton Aminiya.
Da yake martani a taron tabbatar da takarar Kawu Sumaila yau Litinin, Gwamna Abba ya yi gargadin cewa zai fara bude bakinsa yana maida martani ga Kwankwaso idan aka kai shi bango.
Sakon da Abba ya aika wa Kwankwaso
Abba ya ce:
“Mu dai zaman lafiya a Kano shi ne abin da ya fi muhimmanci a gare mu. Amma idan aka kai mu bango, za mu bude baki mu yi magana. Yin shiru ba alamar tsoro ba ce.
“Ko yin shiru ma ibada ce, ba don muna tsoro ba, ba kuma don mu yara ba ne. Ta yaya mutum mai shekara 69 zai kira mai shekara 63 yaro? Girmamawa da ladabi ne kawai saboda ka fi ni shekaru kadan.
“Amma idan dattijo bai mutunta kansa ba kuma bai yi shiru ba, to matashi zai samu abin fada. Don haka muna hada su da Allah da Manzonsa su rufe bakunansu. In ba haka ba, za ku ji abubuwa masu yawa da za mu tona,” in ji shi.

Source: Facebook
Abba ya sasanta Rurum da Kawu Sumaila
A wani labarin, kun ji cewa Gwamna jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sasanta rikicin da ya shiga tsakanin Kabiru Alhassan Rurum da Sanata Kawu Sumaila.

Kara karanta wannan
Magana ta fito, an ji abin da Tinubu ya shirya yi a shekaru 2 na farko bayan ya ci zaben 2027
Rikici ya nemi ya yi kamari a tsakanin manyan wakilan Kano ta Kudu a majalisun tarayyar kasar nan, har an ji Rurum na cewa ya shata layi tsakaninsa da Kawu Sumaila.
Bangarorin biyu sun sanar da cewa sun yafe wa juna tare da warware duk wani sabani da ya shiga tsakaninsu bayan Gwamna Abba ya kashe wutar.
Asali: Legit.ng
