Ana Zargin Tinubu Ya Sake Samun Matsala da Shettima, Zai Iya Shafar Kujeransa
- Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa Bola Tinubu na dab da yanke hukunci kan wanda zai zama mataimakinsa a zaɓen 2027
- Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan makomar Kashim Shettima a zaben shekarar 2027
- Rahotanni sun bayyana cewa wasu a fadar shugaban ƙasa sun nuna rashin jin daɗi bayan Shettima ya raka Hope Uzodinma wajen miƙa fom ɗin takarar Tinubu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Ana hasashen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na shirin bayyana wanda zai kasance mataimakinsa a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Rahotanni sun nuna cewa ana kokarin sasanta rikicin siyasa da ya shafi mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima.

Source: Twitter
Rahoton Punch ya ce hakan na zuwa bayan wasu matsaloli da suka taso tsakanin bangarorin biyu a watannin baya.
Musabbabin dawowar rikicin Tinubu da Shettima
Majiyoyi sun bayyana cewa rikicin ya sake ɓarkewa ne lokacin da shugaban dandalin gwamnoni na APC, Hope Uzodinma, ya karɓi fom ɗin takarar Tinubu domin kaiwa sakatariyar jam’iyyar APC tare da Shettima.
Wasu jami’a a fadar shugaban ƙasa sun nuna rashin jin daɗi kan yadda aka bai wa Shettima damar fitowa fili a wajen miƙa fom ɗin.
Rahotanni sun ce wasu mutane a fadar shugaban ƙasa sun ɗauki matakin bincikar Uzodinma domin tabbatar da biyayyarsa ga tsarin siyasa na shugaban ƙasa.
An bayyana cewa ba a nemi a cire shi daga shugabancin gwamnoni gaba ɗaya ba, sai dai an so a “girgiza shi kaɗan” saboda rawar da Shettima ya taka.
Wata majiya ta ce bayyanar Shettima a wajen miƙa fom ɗin ta sa mutane suka fara tunanin cewa Tinubu ya riga ya amince da shi a matsayin abokin takara na 2027.
Hakan ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin APC, musamman ganin cewa har yanzu ana tattaunawa kan wanda zai dace da kujerar mataimakin shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan
An dora Hayatu Deen a gaban Atiku, Obi da Amaechi a takarar zama shugaban kasa a 2027

Source: Twitter
Ana zargin maye gurbin Shettima a zaben 2027
An ce ana duba yiwuwar maye gurbin Shettima da wasu manyan ‘yan siyasa uku, ciki har da Nuhu Ribadu, Janar Christopher Musa mai ritaya, da tsohon kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara.
Ana ganin zaɓin Dogara ko Musa zai taimaka wajen rage korafe-korafen tikitin Musulmi da Musulmi, cewar Leadership.
Sai dai wasu majiyoyi sun gargadi cewa cire Kashin Shettima daga tikitin APC na iya haifar da babbar matsala a Arewa maso Gabas, inda yake da tasiri sosai.
Sun ce hasarar siyasa da hakan zai jawo na iya fiye da ribar da jam’iyyar za ta samu.
Rahotanni sun kuma bayyana cewa rikicin da ya shafi Uzodinma ya taɓo siyasar gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara.
Tinubu ya magantu kan ikirarin kisan dan ta'adda
Mun ba ku labarin cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da kashe babban kwamanda a kungiyar ISIS, Abu-Bilal Al-Manuki a yankin Tafkin Chadi.

Kara karanta wannan
2027: Tsohon shugaban a INEC ya samu tikiti, zai tsaya takarar gwamnan Yobe a ADC
Tinubu ya ce sojojin Najeriya da taimakon dakarun Amurka ne suka kai samame maboyar yan ta'addan kuma suka samu nasara.
Shugaban kasar ya gode wa Shugaba Donald Trump na kasar Amurka bisa goyon bayan da yake ba Najeriya a yaki da ta'addanci.
Asali: Legit.ng
