Yadda Aka Kama Fasto da Ya Kulla Sace Matan Wasu Malaman Addini a Plateau

Yadda Aka Kama Fasto da Ya Kulla Sace Matan Wasu Malaman Addini a Plateau

  • Wani limamin coci a Jos da wasu jami’an tsaro biyu sun shiga hannun ‘yan sanda bisa zargin shirya sace matan fastoci biyu
  • Bincike ya nuna cewa wani jami’in ruwa ne ya tona asirin shirin, bayan ya ƙi shiga cikin satar saboda imaninsa da tarbiyyarsa
  • ‘Yan sanda sun ce wadanda ake zargin sun amsa laifin, yayin da bincike ke ci gaba domin gano sauran masu hannu cikin shirin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jos, Plateau - Wani shiri da ake zargin an kitsa domin garkuwa da matan fastoci biyu na Cocin Anglican a Jos ya tonu bayan daya daga cikin mutanen da aka dauka aikin ya fallasa shi.

Lamarin ya haifar da muhawara kan barazanar da ake fuskanta daga mutanen da aka amince da su, da kuma yadda kungiyoyin masu aikata laifuka ke amfani da kusancin wasu da al’umma da hukumomin tsaro.

Kara karanta wannan

Zakaran da Allah Ya nufa da cara: Jariri sabon haihuwa da aka sace ya kubuta

An kama fasto yana shirin sace matan fastoci
Fasto Hassan Mijah da sufeta-janar na yan sanda, Rilwan Disu. Hoto: Nigeria Police Force, @zagazOlamakama.
Source: Twitter

Rahotanni daga Zagazola Makama sun ce Rabaran Hassan Yunisim Mijah, mai shekaru 42 daga Tudun Wada da ke Jos ta Arewa, na daga cikin wadanda ake zargi da kitsa shirin.

Ana zargin fasto da shirya garkuwa da mutane

An kama shi tare da Sgt. Ezra Sunday, jami’in Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, da OS Usman Khalid, jami’in Rundunar Sojin Ruwa.

An ce jami’an tsaron biyu suna aiki ne karkashin Sector 1 na Operation Enduring Peace a Jos a lokacin da aka kama su.

Rundunar ’Yan Sandan Plateau ta ce kama mutanen ya biyo bayan samun sahihan bayanan sirri kan wata zargin hada baki domin sace matan Bishop Ephraim Gongden da tsohon Bishop Benjamin Kwashi.

Jami’in da ya tona asirin shirin

Binciken ya fara samun sauyi ne bayan wani jami’in sojan ruwa da ake zargin Mijah ya tuntuba ya ki shiga cikin shirin satar.

Rahotanni sun ce jami’in, wanda aka bayyana a matsayin musulmi mai tsananin bin addininsa, ya sanar da Bishop Ephraim Gongden bayan an tuntube shi domin ya shiga cikin shirin.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: Yadda aka kama dan bindiga yana cire kudin fansa a POS

Jami’in ya ziyarci bishop din a gidansa da ke yankin Rantya, Jos South, inda ya bayyana masa cewa wasu mutane sun tuntube shi domin ya taimaka wajen aiwatar da satar.

Maimakon ya shiga cikin laifin, jami’in ya ce imaninsa da tarbiyyar da ya samu ne suka sa ya ki amincewa da aikin.

Bayan samun wannan bayani, jami’an rundunar ’yan sandan Plateau da ke sashen Vigilance and Criminal Response Unit (VCRU) suka umarci jami’in ya ci gaba da mu’amala da wadanda ake zargin.

Hakan ya ba jami’an damar sanya ido kan shirin tare da kokarin gano cikakken tsarin da ake zargin wadanda ake zargin sun tanada.

An kama fasto da zargin garkuwa da mutane
Taswirar jihar Plateau da ke fama da rashin tsaro. Hoto: Legit.
Source: Original

Yunkurin daukar ’yan bindiga aiki

Masu bincike sun kuma gano wani bangare na shirin da ake zargin ya kunshi yunkurin daukar wata kungiyar ’yan bindiga domin aiwatar da satar.

Rahotanni sun ce Mijah ya fara kokarin daukar wasu ’yan bindiga domin su sace matan biyu, amma yarjejeniyar ta rushe bayan shugaban kungiyar ya bukaci a ci zarafin matan ta hanyar lalata da su yayin da suke tsare.

Bayan wannan yunkuri ya gaza, ana zargin ya nemi wata kungiyar da za ta iya gudanar da aikin, daga bisani ya juya ga jami’an tsaro.

Kara karanta wannan

Duka bayanan da suka fito daga juyin mulkin da aka yi yunkurin yi wa Tinubu

Zargin ya nuna yadda ake iya amfani da hanyoyi daban-daban wajen neman mutanen da ke da damar gudanar da irin wannan laifi.

Fadan kabilanci ya barke a Plateau

Kun ji cewa mutane uku sun mutu sakamakon arangama tsakanin fulani makiyaya da matasan kauyen Mwaghavul da ke Mangu a jihar Filato.

Daya daga cikin wadanda suka mutu dan yankin ne, yayin da biyu makiyaya ne da aka yi rigimar da su.

Sojoji sun shiga tsakani tare da gudanar da samame da amfani da jiragen sama marasa matuki domin tabbatar da tsaro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.