Jerin Masu Neman Takarar Majalisar Tarayya da APC Ta Yi Watsi da Su a Wurin Tantancewa

Jerin Masu Neman Takarar Majalisar Tarayya da APC Ta Yi Watsi da Su a Wurin Tantancewa

Jam’iyyar APC ta fitar da jerin sunayen masu neman takarar kujerar Majalisar Wakilai da ta sanya wa alamar “ba a amince da su ba” a jihohi da dama a Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Daga cikin jihohin da masu neman takara suka gaza tsallake matakin tantance wa a APC akwai Ondo, Bauchi, Ebonyi, Kogi da Rivers.

Shugaban APC.
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda a wurin tantance yan takara a Abuja Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Twitter

Yadda APC ta gudanar da tantancewa

Sunayen na kunshe ne a cikin wata sanarwa da APC ta wallafa a shafinta na X mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam'iyya na kasa, Felix Morka.

Jam'iyyar APC ta bayyana cewa sunayen na daga cikin wadanda ba su tsallake tsarin tantancewar da jam’iyyar ta gudanar domin tabbatar da cancantar su ba a mazabu daban-daban.

Sanarwar ta ce:

“Kwamitocin tantance ‘yan takara na jam’iyyar APC ne suka gudanar da aikin bisa tsarin da dokokin jam’iyyar suka tanada.”

Kara karanta wannan

Takarar 2027: 'Yan APC sun barke da zanga zanga, an yi fashe fashe a Oyo

Masu neman takarar APC ta soke

Sunayen masu neman takara da ba su cancanta ba, wadanda jam'iyyar APC ta fitar yau Asabar, 16 ga watan Mayu, 2026, sun hada da;

Jihar Ondo

1. Hon. Adefisoye Tajudeen (Idanre/Ifedore)

2. Olusegun Victor Ategbole (Akoko South-East/South-West)

3. Seun Oluwashina Ajongbolo (Akoko South-East/South-West)

4. Rt. Hon. Arowole Ayodeji Samuel (Owo/Ose)

5. Morufu Tosin Ibrahim (Akoko North-East/North-West)

6. Oseni Oyeniyi (Akoko North-East/North-West)

7. Olaleye John Adedipe (Akoko North-East/North-West)

Jihar Bauchi

8. Dr. Bashir Ibrahim Bello (Mazabar Darazo/Ganjuwa)

Jihar Ebonyi

9. Hon. Idu Igariwe (Mazabar Afikpo/Edda)

Jihar Kogi

10. Sanni Salau Ogembe (Mazabar Okene/Ogori-Magongo)

Jihar Rivers

11. Air Commodore John Azubuike Opara (mai ritaya) – Mazabar Port Harcourt

12. Hon. Anderson Allison Igbiki – Mazabar Okrika/Ogu-Bolo

13. Awaji Imombek D. Abirite – Mazabar Andoni/Opobo-Nkoro

14. Hon. Boma Goodhead – Mazabar Asari-Toru/Akuku-Toru

APC ba ta bayyana cikakken dalilin da ya sa aka sanya wa wadannan masu neman takara alamar “ba a amince su yi takara ba.”

Kara karanta wannan

2027: Masu neman takara sun cika sakatariyar APC da gidan shugaban jam'iyya

Yadda aka gudanar da zabuka a jihohi

A wani bangare kuma, a jihar Katsina, Jamila Abdu Mani, mai taimaka wa Gwamna Dikko Radda kan harkokin ilimin yara mata, ta lashe zaben fidda gwani na APC na mazabar Mani/Bindawa ta tarayya.

Haka kuma a jihar Adamawa, an samu cikas wajen gudanar da zabukan fitar da gwani na kato bayan kato na Majalisar Wakilai a wasu gundumomi sakamakon rashin isowar jami’an da za su gudanar da zaben.

APC .
Tutar jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Getty Images

Mambobin jam’iyyar APC a Girei, Yola North da Yola South sun shafe sa’o’i suna jira ba tare da samun wani bayani kan fara zaben ba.

Zabukan fitar gwanin APC na daga cikin shirye-shiryen da jam’iyyar le yi domin tunkarar babban zaben 2027.

Jam'iyyu 22 sun cika sharadin INEC

A wani labarin, kun ji cewa hukumar INEC ta tabbatar da cewa jam'iyyun siyasa 22 sun mika kundin rijistar mambobinsu kamar yadda dokar zabe ta 2026 ta tanada.

Kara karanta wannan

NDC: Jam'iyyar su Kwankwaso ta fitar da kudin fom din takarar 2027

INEC ta ce mika kundin rajistar ya biyo bayan karin wa’adin da ta bai wa jam’iyyun siyasa bayan da suka nuna damuwa kan wa’adin farko.

A cewar hukumar, dukkan jam’iyyun siyasar sun mika kundin rajistar mambobinsu a ranar 8 ga Mayu, 2026 ko kafin hakan, kwanaki biyu kafin cikar sabon wa’adin ranar 10 ga Mayu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262