Tsohon Mataimakin Gwamna Ya Samu Tikitin Takara, Zai Kara da Gwamnan Sokoto

Tsohon Mataimakin Gwamna Ya Samu Tikitin Takara, Zai Kara da Gwamnan Sokoto

  • Tsohon mataimakin gwamnan Sokoto ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar ADC domin zaɓen 2027 da ake tunkara
  • Ɗan siyasar ya gode wa Aminu Waziri Tambuwal da sauran shugabanni, matasa, mata da magoya baya bisa goyon bayan da suka nuna masa wajen wannan tafiyar siyasa
  • Ya ce sabon yunkurin ADC zai kawo shugabanci nagari, haɗin kai da manufofin ci gaban jama’a yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ƙara ƙamari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Sokoto - Tsohon mataimakin gwamnan Sokoto ya fito a matsayin ɗan takarar gwamna na sabuwar tafiyar jam’iyyar ADC kafin zaɓen shekarar 2027 a jihar.

Manir Muhammad Dan’iya na daga cikin makusantan tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal a siyasance, ya gode masa bisa goyon baya.

Na kusa da Tambuwal ya samu tikitin takarar gwamna a Sokoto
Tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, Manir Dan'iya da Gwamna Ahmed Aliyu. Hoto: Aminu Waziri Tambuwal Media Office, Director, Media and Publicity Sokoto State.
Source: Facebook

Dan'iya ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da tsohon sakataren yaɗa labaransa, Aminu Abubakar, ya fitar a yau Juma'a 15 ga watan Mayun shekarar 2026 cewar Punch.

Kara karanta wannan

Amaechi ya mika fom din neman takara a ADC, ya fadi a lokacin da zai gyara Najeriya

ADC ta fitar da dan takarar gwamna a Sokoto

Tsohon mataimakin gwamnan, wanda kuma ke riƙe da sarautar Walin Sokoto, ya bayyana wannan nasara a matsayin babban nauyi tare da alƙawarin haɗin kai da ci gaba.

Ya yabawa Aminu Tambuwal saboda goyon baya, shawarwari da gudunmawar da yake bayarwa wajen bunƙasa siyasar Sokoto tare da ci gaban al’ummar jihar baki ɗaya.

Dan’iya ya ce goyon bayan dattawa, matasa, mata da abokan siyasa ya nuna akwai cikakkiyar manufa guda wajen gina makomar Sokoto mai inganci da kwanciyar hankali.

A cewarsa:

“Ina matukar godiya ga Mai Girma, Aminu Waziri Tambuwal, tare da duk masu ruwa da tsaki, abokan siyasa, dattawa, matasa, mata da magoya baya bisa amincewar da suka nuna min.
“Wannan goyon baya babban nauyi ne da nake matukar darajantawa, kuma tare za mu ci gaba da aiki domin hadin kai, zaman lafiya da ci gaban Sokoto."
An fitar da dan takarar gwamnan Sokoto a ADC
Aminu Waziri Tambuwal, Muhammad Dan'iya da Gwamna Ahmed Aliyu. Hoto: @Kafinhausaa, Sokoto State Government.
Source: Facebook

Yadda ADC ta shirya samar da jagoranci nagari

A cewarsa, sabon tafiyar ADC na ƙoƙarin samar da shugabanci mai haɗa kowa, kyakkyawan mulki da manufofin da za su amfani jama’a kafin zaɓen gwamna na 2027.

Kara karanta wannan

Tsohon IGP, Usman Baba, ya janye daga neman takarar gwamnan Yobe a APC, ya fadi dalili

Dan’iya ya kuma roƙi magoya bayan tafiyar da su kasance cikin lumana, haɗin kai da mayar da hankali yayin da tattaunawar siyasa ke ƙara ƙarfi, cewar Daily Post.

Rahotanni sun nuna cewa mutane sama da 10 sun nuna sha’awar neman takarar gwamna a jam’iyyar, ciki har da tsohon jakadan Jordan, Faruk Malami Yabo da sauransu.

Malamin Musulunci ya rasa tikitin takara a Sokoto

Mun ba ku labarin cewa shehin malamin Musulunci, Sheikh Bashir Sani Ahmad Sokoto ya sanar da kansa cewa bai samu tikitin takarar gwamna ba a jam'iyyar ADC.

Malamin ya bayyana haka ne yayin da jam'iyyun siyasa ke kokarin fitar da 'yan takara a hanyar sulhu ko kuma zaben fitar da gwani a Najeriya.

Tun a watan Ramadan ne babban malamin ya ayyana cewa zai tsaya takarar gwamnan Sokoto domin ceto jihar kuma ya kawo cigaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.