Ganduje, Manyan APC Saya wa Abba Fam, An Tara N50m don Takarar Tinubu a 2027

Ganduje, Manyan APC Saya wa Abba Fam, An Tara N50m don Takarar Tinubu a 2027

  • Jiga-jigan APC a Kano sun saya wa gwamna Abba Kabir Yusuf fam domin ya nemi takara gabanin zaben 2027 mai zuwa
  • An kuma amince da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa domin ya samu damar Zarewa zuwa 2031
  • Jam’iyyar ta ce matakin na nufin karfafa hadin kai da tabbatar da nasara a zaben 2027 da a yanzu haka ya tashi yana siyasa tsaye

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano – Jiga-jigan APC a jihar Kano sun saya wa gwamna Abba Kabir Yusuf fam, inda suka ayyana shi a matsayin dan takarar gwamna guda na jam’iyyar a zaben shekarar 2027.

An sanar da wannan mataki ne yayin wani taron jiga-jigan jam’iyyar da aka gudanar a Kano, inda shugabannin jam’iyyar suka tabbatar da cikakken amincewarsu da jagoranci da ayyukan Gwamna Yusuf.

Kara karanta wannan

Mai son takarar gwamna a APC ya ki yarda da zabin Tinubu, ya yi barazanar zuwa kotu

APC ta saya wa Abba Fam na takarar 2027
Abba Kabir Yusuf yana daga fam da APC ta saya masa don sake neman gwamnan Kano a gidan gwamnati Hoto: Hon Salisu Muhammad Kosawa
Source: Facebook

Daily Trust ta wallafa cewa hakan na kunshe a cikin wata sanarwar manema labarai da sakataren yada labaran gwamnan jihar Kano, Mustapha Muhammad, ya fitar a ranar Juma’a 1 ga watan Mayu, 2026.

APC ta tsayar da Abba takarar gwamna a 2027

Politics Nigeria ta wallafa cewa da yake mika fam din a madadin jiga-jigan, tsohon shugaban APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce matakin ya biyo bayan yarjejeniya ta bai daya da aka cimma domin daukar gwamnan a matsayin dan takarar hadin kai.

Ya ce:

"Mun riga mun amince cewa kai ne dan takarar gwamnanmu, kuma domin cika wannan alkawari, ina mika maka wadannan muhimman fam guda biyu — na nuna sha’awar neman takara da na tsayawa takara — domin ka cike su yadda ya kamata ka kuma gabatar.”aisha
Abba ya gode wa APC kan saya masa dan don sake neman takara
Dr. Abdullahi Umar Ganduje yana gaisawa da Gwamna Abba jim kadan bayan mika masa fam na neman takara a gidan gwamnatin Kano Hoto: Hon Salisu Muhammad Kosawa
Source: Facebook

Jiga-jigan sun bayyana cewa sayen fam din wata hanya ce ta nuna jajircewarsu wajen tabbatar da hadin kan jam’iyya da kuma ci gaba da dorewar nasarorin da aka samu a karkashin wannan gwamnati.

Kara karanta wannan

Gwamna Buni da 'yan APC sun fitar da dan takarar gwamnan Yobe a 2027

Sun kara da cewa tsarin dan takara guda zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da sahihin tafiyar zabe a 2027.

2027: An goyi bayan Tinubu a Kano

A nasa bangaren, gwamna Abba Kabir Yusuf ya gode da wannan karamci, inda ya sake jaddada kudirinsa na tafiyar da mulki mai hada kowa da kowa, aiwatar da manufofin da suka shafi talakawa, da kuma ci gaba da bunkasa jihar Kano.

A wani bangare kuma, jiga-jigan APC a Kano sun kuma amince da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa guda na jam’iyyar a zaben 2027, tare da alkawarin bayar da gudummawar Naira miliyan 50 domin sayen fam dinsa.

An cimma wannan matsaya ne a wani babban taro da aka gudanar a dakin taro na Coronation Hall da ke gidan gwamnatin Kano.

Rabiu Sulaiman Bichi ne ya gabatar da kudirin amincewar, wanda dukkannin mahalarta taron suka mara masa baya baki daya.

Shugaban APC na jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, ya bayyana cewa da farko jam’iyyar ta yi tunanin sayen fam din kai tsaye, amma daga bisani ta amince da bayar da gudummawar kudi.

Kara karanta wannan

Tsohon shugaban ƴan sanda ya ƙi yarda da sulhu, ya sayi fom ɗin takarar gwamna

Ya ce:

"Mun amince mu bayar da Naira miliyan 50 domin sayen fam din nuna sha’awa da na tsayawa takara ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

Jiga-jigan sun ce sun dauki wannan mataki ne bisa amincewa da jagorancin shugaban kasa da sauye-sauyen da yake aiwatarwa, tare da kudurin tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaben 2027.

Abba ya magantu kan zaben mataimakin gwamnan Kano

A wani labarin kun ji cewa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kare matakin da ya dauka na nada Hon. Murtala Sule Garo a matsayin mataimakinsa.

Kalaman nasa na zuwa ne bayan majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da nadin da aka yi wa Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin gwamna.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa Murtala Sule Garo ya cancanci mukamin da aka ba shi domin mutum ne da zai iya ba da gudunmawar da ta dace.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng