Jam'iyyar ADC Ta Yi Maganar Hadewa da PRP, Ta Bayyana Shirin da Take Yi
- An yada wasu bayanai masu nuna cewa jam'iyyar ADC mai adawa na shirin hadewa da takwararta ta PRP
- Sakataren yada labarai na ADC, Bolaji Abdullahi, ya fito ya yi karin haske kan batun hadewa da jam'iyyar PRP
- Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa ADC ta mayar da hankali wajen ganin an soke matakin da hukumar INEC ta dauki kan shugabancin jam'iyyar
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Jam’iyyar ADC ta yi martani kan batun cewa tana shirin hadewa da takwararta ta PRP gabanin zaben 2027.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta bayyana cewa ba ta tunanin kulla wani ƙawance da takwararta ta PRP.

Source: Facebook
Hakan na kunshe ne a wani rubutu da sakataren yada labarai na kasa na ADC, Bolaji Abdullahi, ya yi a shafinsa na X a ranar Litinin, 20 ga watan Afirilun 2026.
Ana rade-rade kan ADC
Tun daga ranar 1 ga Afrilu, lokacin da INEC ta soke amincewa da shugabancin ADC ƙarƙashin David Mark ake ta rade-radi kan makomar jam'iyyar.
An yi ta samun rade-radin cewa shugabannin adawa na iya neman haɗewa da wasu jam’iyyun siyasa, ciki har da PRP, gabanin babban zaɓen 2027.
Me ADC ta ce kan hadewa da PRP?
Bolaji Abdullahi ya bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya, inda ya nuna cewa shugabancin haɗakar jam’iyyun ba sa cikin wata tattaunawa da wata jam’iyyar siyasa a halin yanzu.
“Hankalinmu ya karkata ga wani labari da ke yawo cewa jam’iyyar ADC tana tattaunawa da wata jam’iyyar siyasa, musamman PRP sakamakon jiran hukuncin kotu. Muna so mu bayyana karara cewa wannan ba gaskiya ba ne."
- Bolaji Abdullahi
Wane aiki ADC ta tasa a gaba?
Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa haɗakar jam’iyyun tana ci gaba da mayar da hankali ne wajen ƙalubalantar abin da ya kira “matakin sabawa doka” da INEC da wasu da ake zargi wakilan jam’iyya mai mulki ne suka ɗauka a kan shugabancinta.
“Shugabancin haɗakar ba ya gudanar da kowace irin tattaunawa da kowace jam’iyyar siyasa a halin yanzu. Muna da cikakken kudurin tabbatar da cewa matakin sabawa doka da INEC da sauran wakilan jam’iyya mai mulki suka ɗauka a kan shugabancinmu an soke shi."
- Bolaji Abdullahi
Kakakin na ADC ya bayyana cewa jam’iyyar ta yi amanna cewa soke wannan mataki yana da matuƙar muhimmanci wajen kiyaye bin doka da oda da kuma kare tsarin dimokuraɗiyya na jam’iyyu da dama a Najeriya.

Source: Twitter
ADC za ta fadada hadaka
Yayin da yake nanata shirye-shiryensu na faɗaɗa haɗakar domin karɓar wasu ɓangarorin adawa, Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa ADC ba ta tunanin barin dandalinta.
“Duk wata shawara da ke nuna cewa muna tunanin barin ADC magana ce ta hasashe, kuma ya kamata a yi watsi da ita."
- Bolaji Abdullahi
Jam’iyyar ta kuma nuna kwarin gwiwa ga ɓangaren shari’a, inda ta yi kira gare su da su jure duk wani matsin lamba kuma su tsaya tsayin daka wajen kare dimokuraɗiyya.
ADC ta yi wa Tinubu martani
A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar ADC ta yi zazzafan martani ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.
ADC ta bayyana cewa kalaman shugaban suna nuna tsantsar fargaba da damuwa ne maimakon kwarin gwiwar da yake nuna wa a fili.
A cewar ADC, akwai dalilai da dama da ya kamata su jefa shugaban ƙasa a cikin tsoro kafin babban zaɓen 2027.
Asali: Legit.ng


