'Farko Kenan a Najeriya': Tinubu Ya Girgiza da Komawar Manyan Ƴan Siyasa APC daga PDP

'Farko Kenan a Najeriya': Tinubu Ya Girgiza da Komawar Manyan Ƴan Siyasa APC daga PDP

  • Shugaba Bola Tinubu ya ji dadin guguwar siyasa da ta kunno kai a Najeriya da jiga-jigan PDP suka dawo APC
  • Tinubu ya bayyana sauyin jam’iyya daga PDP zuwa APC a Delta a matsayin “guguwar siyasa” mafi girma da aka taba gani
  • Gwamna Sheriff Oborevwori da Ifeanyi Okowa sun ce sauyin ya yi daidai da bukatun Delta, inda suka yaba da kulawar Shugaba Tinubu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Asaba, Delta - Shugaban kasa, Bola Tinubu ya yaba da sauyin jam'iyya da ake samu daga PDP zuwa APC.

Tinubu ya bayyana cewa ba a taba samun irin haka ba a tarihin siyasar Najeriya bayan sauya shekar gwamnan Delta, Sheriff Oborevwori da mukarrabansa.

Tinubu ya ji dadin guguwar siyasa da ta kunno kai a Najeriya
Bola Tinubu ya yaba da zuwan jiga-jigan PDP zuwa APC a Delta. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Rt. Hon. Sheriff Oborevwori.
Asali: Twitter

Tinubu ya magantu da gwamna ya dawo APC

Jawabin Tinubu ya zo ne a wajen bikin sauyin jam’iyya na Gwamna Oborevwori da wasu PDP zuwa APC, a Cenotaph, Asaba da ke jihar Delta, Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin da sauyin jam’iyya daga PDP zuwa APC a Delta ke tayar da kura, Shugaba Tinubu ya ce hakan ba a taba ganin irinsa ba.

Sauyin jam’iyyar Sheriff Oborevwori da Ifeanyi Okowa da sauran manyan PDP ya kawo karshen mulkin PDP da ya dauki kusan shekara 26 a jihar.

Jiga-jigan da suka karɓi gwamna zuwa APC

Wadanda suka karbi sababbin 'yan APC sun hada da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Tinubu da Abdullahi Umar Ganduje da wasu gwamnoni.

Har ila yau, akwai Sanata Omo-Agege, Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, da Sanata Nwoko, Onowakpo-Thomas da sauransu.

Tinubu ya ce:

“Me ya fi wannan rana alfanu? Wannan guguwa ce ta siyasa da ba a taba gani ba a Kudu maso Kudu da kasar nan.
“Guguwa ce ta siyasa inda duk Sanatoci daga jihar suke APC, hakan ba a taba ganin irinsa ba a tarihin siyasar Najeriya.”

“’Yan Majalisar Wakilai da Gwamna da kwamitinsa da kansiloli kananan hukumomi 25 duk sun sauya sheka."
Tinubu ya magantu bayan tururuwa zuwa APC daga PDP
Bola Tinubu ya ce ba a taba samun guguwar siyasa irin wannan karo ba. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Tinubu ya yaba da alaƙar Okowa, Oborevwori

Tinubu ya yaba wa tsohon gwamna Okowa bisa kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da magajinsa, yana mai kiransa babban shugaba, cewar Tribune.

A martaninsa, Gwamna Oborevwori ya ce:

“Sauyinmu zuwa APC ba na Delta kawai ba ne, na kasa baki daya ne, na yi imani da cewa wasu gwamnoni ma za su biyo baya. Idan kana da shiri, ba za ka kasa ba.
“Delta ba za ta tsaya a baya ba. Muna cikin adawa sama da shekaru 10. Shugaba ya nuna mana kauna, za mu rama.

Gwamna ya yi wa Tinubu alƙawarin miliyoyin kuri'u

Kun ji cewa gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa APC tare da alkawarin kawowa Bola Tinubu kuri'u miliyan 1.4.

Oborevwori da mataimakinsa Monday Onyeme da tsohon gwamna Ifeanyi Okowa da sauran jiga-jigan PDP sun koma APC a jihar Delta gaba ɗaya.

Rahotanni suka ce sauyin zai ƙarfafa APC a yankin Kudu maso Kudu, amma masana suna ganin samun kuri'un da gwamnan ke fata zai yi wahala.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.