2027: Ta Yiwu Dan Takarar Shugaban Kasa Ya Hade da El-Rufai, Hadimin Atiku Ya Magantu

2027: Ta Yiwu Dan Takarar Shugaban Kasa Ya Hade da El-Rufai, Hadimin Atiku Ya Magantu

  • Yayin da ake ta shirin siyasar 2027, an yi hasashen cewa dan takarar shugaban kasa a LP, Peter Obi zai hade da Nasir El-Rufai a jam’iyyar SDP
  • Kakakin kamfe na dan takarar shugaban kasa a PDP, Atiku Abubakar shi ya bayyana haka a yau Juma’a 22 ga watan Maris a shafin X
  • Daniel Bwala ya ce Obi zai bar jam’iyyar LP ne yayin da kungiyar NLC ke kokarin kwace ragamar shugabancin jam’iyyar gaba daya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja – Daniel Bwala, Kakakin kamfen dan takarar shugaban kasa a PDP, Atiku Abubakar ya ce akwai yiwuwar ruguntsumin siyasa a kwanakin nan.

Bwala ya ce dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai su na shirin hadewa saboda zaben 2027.

Kara karanta wannan

Ribadu, FFK zuwa Ningi: El-Rufai ya ruda APC, ya tada kura kwatsam a siyasar Najeriya

An yi hasashen dan shugaban kasa zai hade da El-Rufai kan zaben 2027
Bwala ya yi zargin Peter Obi zai hade da El-Rufai kan zaben 2027. Hoto: Peter Obi, Nasir El-Rufai.
Asali: Facebook

Wani hasashe aka yi kan Obi, El-Rufai?

Bwala ya ce Obi zai watsar da jam’iyyar LP zuwa SDP saboda rikicin shugabanci da jam’iyyar tasa ke fuskanta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jagoran na APC a yau ya bayyana haka ne a shafinsa na X inda ya ce El-Rufai ya na shirin barin jam’iyyar APC mai mulkin kasar.

“Ana zargin Peter Obi zai hade da Nasir El-Rufai a jam’iyyar SDP yayin da kungiyar NLC ta shirya kwace shugabancin jam’iyyar LP.”
“Ruguntsumin siyasa zai faru a wannan kwanakin amma babu abin da zai hana Shugaba Tinubu barci wanda ya san lungu da sakon siyasa.”

- Daniel Bwala

Jita-jitar ficewar El-Rufai daga APC

Wannan hasashe ya biyo bayan jita-jitar da ake yadawa cewa tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai zai bar jam’iyyar APC.

Hakan ya biyo bayan ziyarar sa tsohon gwamnan ya kai a ofishin jam'iyyar SDP a birnin Abuja.

Kara karanta wannan

Gaskiya ta bayyana: Jigon LP ya bayyana dalilin da yasa Peter Obi ya yi buda-baki da Musulmai

Jita-jita yayin da Ribadu ya ziyarci El-Rufai

A baya, mun ruwaito muku cewa hadimin Shugaba Tinubu a bangaren tsaro, Nuhu Ribadu ya ziyarci tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Ribadu ya kai ziyarar ce yayin da ake yada jita-jitar cewa El-Rufai na shirin watsi da jam’iyyar APC yayin da ake tunkarar zaben 2027.

Asali: Legit.ng

Online view pixel