Bayan Abin da Ya Faru, Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Musa Lukuwa
- Gwamnatin Jihar Sokoto ta bayar da umarnin rufe Masallacin Juma’a na Sheikh Musa Lukuwa da ke Mabera bayan harin da ya yi sanadin kisa
- Gwamnatin ta kafa kwamitin malaman addinin Musulunci domin binciken musabbabin rikicin da kuma hanyoyin hana sake faruwar lamarin
- An bayyana masallacin a matsayin wurin da aka aikata laifi, kuma zai ci gaba da kasancewa a rufe har sai an ba da wani sabon umarni
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Sokoto, Nigeria - Gwamnatin Jihar Sokoto ta bayar da umarnin rufe Masallacin Juma’a na Sheikh Musa Lukuwa da ke Mabera, cikin birnin Sokoto, bayan abin da ya faru a masallacinnwanda ya yi sanadin kisa.
Gwamnatin ta kuma kafa wani kwamiti na malaman addinin Musulunci domin binciken musabbabin lamarin na kusa da na nesa, tare da ba ta shawarar matakan da suka dace domin hana sake faruwar irin wannan abu.

Source: Facebook
Dalilin rufe masallacin Sheikh Lukuwa
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Gidan Gwamnatin Sokoto, Abubakar Bawa, ya fitar ranar Talata.
Ya ce masallacin da gwamnati ta bayyana a matsayin wurin da aka aikata laifi zai ci gaba da kasancewa a rufe har sai an ba da wani sabon umarni.
Matakin ya biyo bayan tashe-tashen hankulan addini da aka samu a wasu sassan birnin Sokoto, ciki har da rahoton daba wa wani malamin addinin Musulunci, Malam Musa Lukuwa, wuka jim kadan bayan ya jagoranci sallar Juma’a a masallacin.
Gwamnati ta kafa kwamitin bincike
Gwamnatin ta ce kwamitin zai binciki abubuwan da suka jawo tashin hankalin tare da gabatar da shawarwari domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
Haka kuma, ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan harin da kuma kisan da ya biyo baya a masallacin.
Gwamnatin Sakkwato ta kuma nisanta kanta daga duk wani mutum, ba tare da la’akari da matsayinsa ba, da ke fakewa da addini domin zagon kasa ko nuna rashin girmamawa ga Annabi Muhammad (SAW), iyayensa, iyalansa da sahabbansa.

Source: Facebook
Gwamnatin Sakkwato ta dauki matsaya
Ta sake tabbatar da “cikakkiyar biyayya da girmamawa” ga Annabi, iyayensa, iyalansa da sahabbansa, tare da kira ga mazauna jihar da su ci gaba da nuna masa kauna da tausayi.
Gwamnatin ta roki mazauna jihar da su guji yin kalaman tunzura jama’a da ka iya kawo cikas ga zaman tare cikin lumana da Sokoto ta shahara da shi.
Ta kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa ta kuduri aniyar kare rayuka da dukiyoyin kowane dan kasa a jihar.
MURIC ta yi Allahi wadai da lamarin
A wanai labarin, kun ji cewa ƙungiyar MURIC ta yi Allah wadai da harin da aka kai wa Sheikh Musa Lukuwa da kuma zargin kashe wanda ake zargi da kai harin.
MURIC ta kuma soki hukumomin tsaro da na gwamnati bisa zargin gaza ɗaukar matakan da suka dace tun da wuri kan abin da ta bayyana a matsayin kalamai masu kawo cece-ku-ce da malamin ya riƙa yi.
Asali: Legit.ng

