Babbar Magana: Amurka Ta Shigo da Manyan Makamai da Kayan Aiki cikin Najeriya

Babbar Magana: Amurka Ta Shigo da Manyan Makamai da Kayan Aiki cikin Najeriya

  • Amurka ta bai wa Rundunar Sojin Sama ta Najeriya kayan aikin soja domin taimakawa ƙasar wajen yaƙi da ta’addanci a Arewacin Najeriya
  • An kawo kayan wadanda suka kunshi maiamai a ranar Lahadi, 6 ga watan Satumba, 2026 ta cikin jirgin sojin saman Amurka C-17
  • Isowar kayan ya zo ne wata guda bayan tawagar Najeriya karkashin jagorancin NSA Nuhu Ribadu ta halarci taron hadin gwiwa a Washington DC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Ƙasar Amurka ta kawo kayan aiki da suka kunshi makamai da sauransu ga Rundunar Sojin Sama ta Najeriya.

Amurka ta shigo da kayan aikin soja Najeriya ne wata guda bayan mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa birnin Washington DC.

Kayan aiki.
Kayan aikin sojojin sama da Amurka ta kawo Najeriya Hoto: @nigeriastories
Source: Twitter

Jaridar Nigeria Stories ta wallafa hotunan kayan aikin da Amurka ta shigo da su Najeriya domin tallafa wa rundunar sojojin sama wajen yaki da kungiyoyin yan ta'adda a shafinta na X.

Kara karanta wannan

Asiri ya fara tonuwa: An kama mutum 2 kan kashe Danshagamu a Kano

Hakan ne na zuwa ne bayan tawagar Najeriya da Amurka sun yi wata ganawa ta kwamitin hadin gwiwar kasashen biyu kan tsaro a Washington DC.

An kawo kayan aikin ne ranar Lahadi, 6 ga watan Satumba, ta cikin wani jirgin sojin saman Amurka kirar C-17.

Kayan aikin na cikin yarjejeniyar sayar da kayan aikin soja tsakanin ƙasashen biyu, wadda ke ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar Amurka da Najeriya.

Haka kuma, kayan za su taimaka wa Najeriya wajen ƙoƙarin da take yi na yaƙi da ta’addanci a arewacin ƙasar.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262