Mata na cikin Alheri, An Fara Raba Tallafin N50,000 ga Wadanda Suka Cancanta a Jihar Kano

Mata na cikin Alheri, An Fara Raba Tallafin N50,000 ga Wadanda Suka Cancanta a Jihar Kano

  • Gwamnatin jihar Kano ta raba tallafin Naira miliyan 290 ga mata 5,800 a kananan hukumomi 44 domin fargadi da sana'o'in su
  • Rahotanni sun nuna cewa kowace mace daga cikin matan za ta samu N50,000 domin fara ko fadada sana'arta
  • Gwamna Abba Oabir Yusuf ya ce za a ci gaba da biyan tallafin da wadanda suka cancanta har zuwa watan Disamba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da fara rabon tallafin Naira miliyan 290 ga mata 5,800 a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

An bayar da tallafin ne karkashin shirin gwamnati na karfafa mata da rage talauci da ake gudanarwa duk wata.

Abba.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yana jawabi a fadar gwamnati Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Gwamna Abba Yusuf ya kaddamar da sabon zagaye na shirin a Open Arena da ke gidan gwamnatin Kano ranar Litinin, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Atiku ya ɗauki zafi da ya ga rahoton yadda aka raba tallafin N25,000 ga yan Najeriya

Ya ce kowace daga cikin matan da za su amfana da shirin za ta samu N50,000 domin fara sabuwar sana'a ko fadada wadda take yi.

Yadda za a raba tallafin ga matan Kano

Gwamna Abba ya bayyana cewa an gayyaci kashi 20 cikin 100 na wadanda suka amfana daga kowace karamar hukuma domin halartar bikin kaddamar da shirin.

Ya ce sauran kashi 80 cikin 100 za su karbi tallafinsu a kananan hukumominsu.

"Yau muna kaddamar da tallafi ga mata 5,800 daban-daban. Daga cikin wadannan mata 5,800, mun zabo kashi 20 daga kowace karamar hukuma domin halartar wannan bikin kaddamarwa.

"Gobe, kowane shugaban karamar hukuma da mambobin kwamitinsa za su koma kananan hukumominsu domin raba tallafin ga sauran kashi 80."

Gwamna Abba ya yi bayani kan shirin

Gwamna Abba ya ce shirin karfafa mata ya fara tun bayan hawansa mulki, sai dai ya ce an dakatar da shi na wani dan lokaci yayin sauyin gwamnatin zuwa jam'iyyar APC.

Kara karanta wannan

Kano da wasu jihohi 7 da cutar 'Diphtheria' ta fi kama mutane, NCDC ta gano matsalar

A cewarsa, an dakatar da shirin ne domin sake tsara shi tare da tabbatar da cewa matan da suka yi rajista tun farko, da kuma wadanda suka shiga APC, sun shiga cikin wadanda za su amfana.

Gwamnan ya tabbatar wa mata cewa gwamnati ta ware kudaden da za a ci gaba da gudanar da shirin, yana mi cewa za a ci gaba da biyan tallafin har zuwa watan Disamba.

Gwamna Abba Yusuf ya bukaci wadanda suka amfana da tallafin su yi amfani da kudaden wajen sana'o'in da za su amfane su.

Gwamna Abba.
Gwamnam jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yayin da ya oarbi bakuncin wasu magoya baya a gidan gwamnati Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Ya ba da misalin kananan sana'o'i da kasuwanci, musamman sayar da kayan masarufi da abinci. Ya ce hakan zai taimaka wa matan wajen dogaro da kansu tare da tallafa wa iyalansu.

Gwamnan ya kuma nemi mata su goyi bayan 'yan takarar APC a zaben 2027, inda ya bukace su da su zabi 'yan takarar shugaban kasa, gwamna, majalisar tarayya da majalisar dokokin jiha na APC.

Gwamnatin Tinubu za ta kara raba tallafi

A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta hannun hukumar SMEDAN ta sake bude shirin ba da tallafin N50,000 ga kananan 'yan kasuwa a Najeriya.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya ware gwamnonin Arewa, ya fadi matsalan da za su fuskanta a zaben 2027

Hukumar ta bayyana cewa wannan shirin ya bambanta da Presidential Conditional Grant Scheme, duk da cewa dukkansu na bayar da tallafin N50,000 ga kananan sana'o'i.

Abba ya ba da kwangilolin kusan N1trn

Kun ji cewa gwamnatin Kano ta ce ta ba da kwangilolin ayyuka na N996.29bn a karkashin gwamnatin Abba Kabir Yusuf, inda aka kammala ayyuka 867 a fadin jihar.

Gwamnatin ta kuma ce ba ta karbo ko sisi a matsayin bashi, daga cikin gida ko wajen Najeriya, domin daukar nauyin ayyukan da aka aiwatarnba, yayin da aka soke kwangiloli biyar saboda karya yarjejeniya

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262