Gwamna Abba Ya Yi Magana Mai Tsauri kan Kisan Fitaccen Mai Sharhi kan Siyasa a Kano

Gwamna Abba Ya Yi Magana Mai Tsauri kan Kisan Fitaccen Mai Sharhi kan Siyasa a Kano

  • Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi Allah-wadai da kisan gillan da aka yi wa fitaccen dan soshiyal midiya Ibrahim Khalil, wanda aka fi sani da Danshagamu
  • Gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta gano tare da kama wadanda ke da hannu a kisan domin doka ta yi aiki a kansu
  • Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su kwantar da hankula, tare da kauce wa ɗaukar doka a hannu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria – Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa fitaccen mai amfani da kafafen sada zumunta kuma mai sharhi kan harkokin siyasa, Ibrahim Khalil, wanda aka fi sani da Danshagamu.

Gwamna Abba ya umarci jami’an tsaro da su gaggauta gano tare da kama dukkan wadanda suke da hannu a aikata kisan domin a gurfanar da su a gaban doka.

Kara karanta wannan

Magana ta girma: Amnesty ta shiga lamarin kisan Ɗan Shagamu a Kano

Abba.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yama jagorantar taron Majalisar zartarwa ta jiha Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Facebook ranar Laraba, 9 ga watan Satumba, 2026.

Yan uwa marigayin sun ce wasu mutane da har yanzu ba a gano su ba sun kai wa marigayin hari bayan sun kutsa gidansa, inda suka yanka shi har lahira.

Rundunar yan sandan Kano ta ce ta kama mutum biyu da ake zargin sune suka kashe Danshagamu.

Gwamna Abba ya yi magana

Sai dai da yake martani, Gwamna Abba ya bayyana kisan a matsayin abin ban tsoro da ba za a amince da shi ba, yana mai nuna damuwa kan yanayin da lamarin ya faru.

Ya kuma bukaci a gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da cewa an gurfanar da duk wadanda ke da hannu a lamarin a gaban kuliya.

Gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin da abokansa da kuma abokan hulɗarsa, yana addu’ar Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya kuma ba shi hutawa ta har abada.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya dauki zafi kan kisan Dan Shagamu, ya sha babban alwashi

Gwamna ya kwantar da hankulan jama’a

Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar Kano da su kwantar da hankula tare da kauce wa ɗaukar doka a hannu.

Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatin za ta ci gaba da aiki tare da jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kano.
Ibrahim Khalil Danshagamu da mai girma gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Haka kuma, Gwamna Abba ya umarci hukumomin tsaro da abin ya shafa, musamman Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) da ’yan sandan Najeriya na jihar Kano, da su ƙara kaimi wajen gano, kama da gurfanar da wadanda suka aikata kisan.

Ya jaddada cewa ba za a bari wani mutum ko wata ƙungiya ta ɗauki doka a hannunta ba.

Kwankwaso ya bukaci a dauki mataki

Kun ji cewa Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana matuƙar damuwarsa kan kisan shahararren mai sharhin siyasa a kafafen sada zumunta, Ibrahim Khalil Dan Shagamu.

Ya ce Dan Shagamu ya mutu ne sakamakon mummunan hari, inda ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta gaggauta kafa kwamitin bincike domin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: