An Kalubalanci Tinubu Ya Yi Tafiya a Mota Idan ya Gamsu da Tsaro a Najeriya

An Kalubalanci Tinubu Ya Yi Tafiya a Mota Idan ya Gamsu da Tsaro a Najeriya

  • Jam'iyyar APM ta kalubalanci shugaban kasa Tinubu da ministan tsaro Gen. Christopher Musa (retd.) su yi tafiya a kan hanya ba tare da dakaru ba
  • Jam'iyyar ta mayar da martani ne kan kalaman ministan da ya ce an murkushe 'yan ta'adda kuma sace mutane a yanzu ya koma wata matsalar zamantakewa
  • Sakataren yada labarai na jam'iyyar, Abubakar Yusuf, ya ce gwamnatin na tsallake gaskiya ne kawai game da matsalar tsaro a kasar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abuja - Jam'iyyar APM ta kalubalanci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Ministan Tsaro, Gen. Christopher Musa (retd.), da sauran manyan jami'an gwamnati da su yi tafiyar mota a kan hanya ba tare da jami'an tsaro ba idan har da gaske tsaro ya inganta.

Jam'iyyar ta fitar da wannan kalubale ne a ranar Asabar a birnin Abuja yayin da take maida martani kan ikirarin da Musa ya yi kwanan nan na cewa Gwamnatin Tarayya ta "ci galaba kan 'yan ta'adda" kuma sace mutane ya zama wata matsalar zamantakewa maimakon babbar matsalar tsaro.

Kara karanta wannan

2027: Jam'iyyar NDC ta su Kwankwaso ta fitar da sunayen yan takarar gwamna a jihohi 12

Sakataren yada labaran jam'iyyar ta APM na kasa, Mr Abubakar Yusuf, ya zargi gwamnatin Tinubu da rayuwar karya kan ainihin halin da ake ciki, inda ya bayyana cewa abin da ke faruwa a kasa ya saba da da'awar gwamnatin.

Ka yi tafiya a mota idan ka gamsu da tsaron kasar nan, APM
Yadda aka kalubalanci Tinubu kan tsaro | Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/APM
Source: Facebook

Abin da Jam'iyyar APM ke cewa

Da yake martani kan yadda tsaro yake a Najeriya, Yusuf ya ce:

"Idan har tsaro ya inganta kamar yadda gwamnatin ke ikirari, APM tana kalubalantar Shugaban Kasa, Ministan Tsaro da sauran manyan jami'an fadar shugaban kasa da su yi tafiyar mota ba tare da jami'an tsaro ba kamar yadda sauran 'yan Najeriya ke yi."

'Yan Najeriya da dama sun bayyana rashin jin dadinsu kan yadda gwamnatin kasar ke ci gaba da magana kan ingancin tsaro, inda a har yanzu ake fama da matsanancin rashin tsaro.

Batun da ya tada kura a Najeriya

Minista Musa, yayin da yake magana a wata hira da gidan talabijin a ranar Talata, ya ce gwamnati ta sami nasarori wajen yakar ta'addanci kuma matsalar ta ragu.

A cewarsa:

"Gaskiya ne cewa munci galaba kan 'yan ta'adda saboda yanzu hare-haren ba su da yawa, abin da ake fama da shi yanzu shi ne sace mutane.

Kara karanta wannan

"Ka yi yadda na yi," Atiku ya sake kinkimo magana mai girma kan bayanan Tinubu na Amurka

"Sace mutane wata matsala ce ta zamantakewa inda yanzu za ka ga mata na sace mazajensu ko maza na sace 'ya'yansu."

Ministan ya ci gaba da cewa:

"Ina tabbatar muku cewa tsaro ya inganta. Watakila ka lura cewa ba ka cika jin hare-haren Boko Haram ko ISWAP a ko'ina ba, sai dai jifa-jifa."

Ana zaman dar-dar a Najeriya

Sai dai, a zahirin gaskiya tsaro bai inganta ba a Najeriya, saboda har yanzu 'yan kasar na ci gaba da zaman dar-dar a kusan dukkan yankunan kasar.

Wakilin Legit.ng Hausa ya tattauna da wata 'yar kasuwa mai gudanar da hada-hadar saye da sayarwa tsakanin Gombe da Taraba, Sadiya Muhammad, inda ta shaida mana cewa:

"Gaskiya tsaro kam babu a Najeriya. Kullum idan na hau mota a Gombe zan tafi Taraba hankali na a tashe yake don ban san me zai faru ba. Fatanmu Allah ya kawo mana sauki cikin gaggawa."

Atiku ya sha alwashin kawo tsaro

A bangare guda, dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar ya bayyana aniyarsa na tabbatar da tsaro a Najeriya.

Kara karanta wannan

Trump ya gano wadanda suke son ƙasar musulunci ta Iran ta yi nasara kan Amurka

Ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da BBC Hausa, inda ya kushe wasu manufofin gwamnatin Tinubu.

Ya kuma yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi jin dadin 'yan kasa, ciki har da dawo da tallafin man fetur.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng