An Shiga Yanayin Tashin Hankali da Wani Bam Ya Tashi da Mutane a Jihar Zamfara
- Rahotanni sun nuna cewa mutane biyu sun mutu bayan wani abin fashewa da ake zargin bam nd ya tashi a hanyar Gurusu-Gwashi ta jihar Zamfara
- Majiyoyi daga yankin da lamarin da auku sun bayyana cewa ana zargin wani babur ne ya taka bam ɗin da aka binne a ƙasa a Bukuyyum
- Dakarun rundunar sojoji sun ci gaba da sintiri da mamaye yankin domin hana sake kai makamancin wannan hari da kuma bincike wurin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Zamfara, Nigeria - Mutane biyu sun rasa rayukansu bayan wani bam da aka dasa, wato IED, ya tashi a hanyar Gurusu-Gwashi da ke ƙaramar hukumar Bukuyyum ta jihar Zamfara.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:04 na safiyar jiya Laraba, 26 ga watan Augustan 2026, kamar yadda majiyoyin tsaro suka tabbatar.

Source: Original
Masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a Najeriya Zagazola Makama, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani rahoto da ya wallafa a shafinsa na X.
Majiyoyin tsaro sun shaida wa Makama cewa dakarun runduna ta 1 da aka jibge a sansanin FOB da ke Gwashi sun gaggauta mayar da martani bayan samun rahoton fashewar bam ɗin.
Yadda babur ya taka bam a Zamfara
Rahotanni sun ce binciken farko da jami'an tsaro suka gudanar ya nuna cewa wani babur ne ya taka bam ɗin da aka binne a yankin, lamarin da ya haddasa fashewar mai ƙarfi.
A cewar majiyoyin, fashewar bam din ta yi sanadin mutuwar wani namiji da wata mace da ke wurin.
An gano gawarwakin mutanen biyu a wurin da lamarin ya faru, kafin daga bisani a kwashe su zuwa Babban Asibitin Bukuyyum domin gudanar da matakan da suka dace.
Sojoji sun kai dauki cikin gaggawa
Zagazola Makama ya nakalto wata majiya tana cewa jami'an tsaro sun fara gudanar da bincike domin gano cikakken bayani kan yadda aka dasa bam ɗin da kuma waɗanda ka iya kasancewa suna da hannu a lamarin.
Bayan fashewar, dakarun sojin sun ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin, inda suka ci gaba da mamaye wurin tare da gudanar da sintiri a kan hanyar da kuma wuraren da ke kewaye.
Matakan na daga cikin ƙoƙarin da jami'an tsaro ke yi na hana sake kai hare-hare da kuma hana 'yan bindiga da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuffika samun damar gudanar da ayyukansu a yankin.

Source: Twitter
Hare-haren bam sun ƙaru a Zamfara
Jihar Zamfara, wadda ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, ta fuskanci hare-haren 'yan bindiga da kuma amfani da na'urorin fashewa a wasu hanyoyi da yankunan karkara.
Hare-haren bam na daga cikin barazanar da ke jefa tsoro a zukatan mazauna yankunan, musamman matafiya da jami'an tsaro da ke amfani da hanyoyin da ke tsakanin garuruwa da ƙauyuka.
A watan Yuni, wasu jami'an 'yan sanda uku sun rasa rayukansu bayan wani bam na IED ya tashi a hanyar Anka zuwa Bagega, a ƙaramar hukumar Anka ta jihar Zamfara.

Kara karanta wannan
Wani mutumi ya zare bindiga, ya buɗe wa mutane wuta a wurin bikin aure a jihar Kano
Sojoji sun ceto mutane a Zamfara
Kun ji cewa Sojojin Operation Fansan Yamma sun kubutar da wasu bayin Allah, daga cikinsu har da jariri, daga hannun ’yan bindiga da suka kai wani hari a Zamfara.
An kuma bayyana cewa mata biyu sun samu raunukan harbin bindiga a lokacin harin, kuma an garzaya da su asibiti.
Asali: Legit.ng

