Atiku Ya Dauki Zafi, Ya Sake Fallasa Abin da Yan Najeriya ba Su Sani ba kan Tallafin Man Fetur
- Dan takarar shugaban kasa na ADC Atiku Sbubakar ya ce babu abin da zai hana shi dawo da tallafin mai da ya yi wa ’yan Najeriya alkawari
- Ya zargi gwamnatin Tinubu da cewa tana kiran cire tallafin mai gyara tattalin arziki tare da bai wa masu zuba jari a man fetur rangwame
- Ya nemi gwamnati ta bayyana wadanda suka ci gajiyar rangwamen harajin man fetur da kudaden shiga da aka yi watsi da su
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce babu sbin da Shugaba Bola Tinubu ko miliyoyin ’yan tawagarsa za su fada d zai za ya janye yunkurinsa na dawo da tallafin mai.
Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC, ya zargi gwamnatin Tinubu da kiran cire tallafin mai da sunan gyara tattalin arziki, yayin da take ci gaba da bai wa yan kasuwar fetur rangwamen haraji da wasu fa’idodi.

Kara karanta wannan
Jigo a APC kuma dan kasuwar mai ya kwancewa Atiku zani kan dawo da tallafin fetur

Source: Facebook
Vanguard ta rahoto cewa madugun adawar ta Najeriya ya fadi jaka ne a cikin wata sanarwa da Babban Mataimakinsa na Musamman kan Hulda da Jama’a, Phrank Shaibu, ya fitar a Abuja ranar Lahadi.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce ikirarin Tinubu na cewa ya cire tallafin mai yaudara ce kawai, domin yana biyan tallafi amma da sunan rangwamen haraji da sauran abubuwan ƙarfafa gwiwa ga dillalan mai.
Atiku ya kafa hujjarsa ne kan bayanan asusun binciken kuɗaɗen da kamfanin mai na kasa (NNPC) ya fitar, yana mai cewa alkaluman sun saɓa da ikirarin gwamnati na cewa an kawo ƙarshen tallafin mai.
Atiku ya fasa kwai kan bayanan NNPCL
A cewar sanarwar, asusun NNPC na 2023 ya nuna an kashe kusan Naira tiriliyan 4.84 a matsayin kuɗaɗen tsaron makamashi da gibin da ya danganci hakan.
Ya ce a cikin bayanan kashe kuɗaɗe na kamfanin NNPC da aka tantance na 2024 kuma, an samu kusan Naira tiriliyan 7.13 a ƙarƙashin kuɗaɗen tsaron makamashi.
Ya ce a sauƙaƙe, gwamnati tana ci gaba da biyan wani bangare na farashin fetur yayin da gefe guda Tinubu ya sanar cewa an kawo ƙarshen tallafin mai.
“Ko gwamnati ta kira shi tallafi ko wani abu daban, mun ssn an yi amfani da kuɗaɗen gwamnati wajen cike gibin da ke tsakanin ainihin kuɗin da man ya ci da kuma farashin da ake sayar da shi,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ba za a iya cewa an soke tallafin mai a bainar jama’a sannan a sake bayyana shi a cikin asusun gwamnati da wani suna daban ba.

Source: Twitter
Atiku ya bayyana tsarinsa
Atiku ya bayyana shirin nasa mai suna Atiku Economic Recovery Plan a matsayin wanda ya bambanta da tsohon tsarin tallafin mai da ya kira “mai cike da rashin gaskiya da cin hanci da rashawa”.
Ya ce shirins na dawo da tallafin mai zai kasance da iyaka bayyananniya, kasafin kuɗi a fili da sa ido mai zaman kansa, kamar yadda Punch ta rahoto.
Hadimin Atiku ya soki cire tallafin mai
Kun ji cewa mai magana da yawun ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar, Kenneth Okonkwo, ya soki cire tallafin man fetur.
Okonkwo ya ce cire tallafin bai kawo sauƙin rayuwa ga 'yan Najeriya ba, yana mai cewa tsadar man fetur, hauhawar farashin kayayyaki da faduwar darajar Naira sun ƙara tsananta wahalhalun jama'a.
Asali: Legit.ng
