Gwamnan Kebbi Ya Kirkiro Sabuwar Masarauta, Ya Yi Sababbin Nade Nade
- Gwamnan jihar Kebbi, Dr Nasir Idris, ya amince da kafa sabuwar gunduma mai kunshe da yankunan kauyuka takwas a karamar hukumar Dandi
- Dr. Nasir Idris ya kuma amince da nada sabon mai unguwa a karamar hukumar Augie domin karfafa tsarin mulkin gargajiya da inganta shugabanci a matakin kasa
- Gwamnan ya kuma nada mutumin da zai jagoranci sabuwar gundumar da aka kafa domin gudanar da harkokin mulki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kebbi - Gwamnan Jihar Kebbi, Dr Nasir Idris, ya amince da kafa sabuwar gunduma mai kunshe da yankunan kauyuka takwas a karamar hukumar Dandi ta jihar.
Gwamnan ya kuma amince da nada sabon mai unguwa a karamar hukumar Augie, a wani mataki na karfafa hukumomin gargajiya da inganta shugabanci a matakin kasa.

Source: Facebook
Gwamna Nasir ya yi nade-nade
Kwamishinan Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, Alhaji Garba Umar Dutsinmari, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Birnin Kebbi ranar Alhamis, 13 ga watan Agustan 2026, cewar rahoton jaridar The Punch.
A cewar kwamishinan, an kafa sabuwar gundumar Buma ne daga tsohuwar gundumar Dolekaina da ke karamar hukumar Dandi, inda aka nada Alhaji Salisu Hakimi a matsayin shugaban gundumar.
Gundumar Buma ta kunshi yankunan kauyuka takwas da suka hada da Tunga Rafi, Gamana, Tudunsan, Gillare, Bump Town, Goraro, Bukki da Alfarma Kwara.
An nada sabon shugaban kauye
Gwamna Idris ya kuma amince da nada Nasiru Umar Maizabo a matsayin mai unguwar Marafan Garin Haruna da ke gundumar Tiggi a karamar hukumar Augie.
Dutsinmari ya ce an yi nade-naden ne bisa tanadin dokar kananan hukumomin Jihar Kebbi ta shekarar 2008, musamman sashe na 10, karamin sashe na (A) da (B), wadanda suka bai wa gwamnati ikon kafa gundumomi da nada shugabannin gundumomi.
An ba su shawara
Kwamishinan ya bukaci sababbin masu sarautar gargajiyar da aka nada da su tabbatar da bin doka da oda, gaskiya, rikon amana da kuma sadaukarwa wajen gudanar da ayyukansu.
“An yi nadinku ne bisa la’akari da tarihin ayyukanku na baya. Ku kasance da tabbacin cewa gwamna da ma’aikatar za su ba ku cikakken goyon baya da hadin kai.” In ji shi
Ana sa ran wannan mataki zai karfafa hukumomin gargajiya tare da inganta gudanar da mulki a matakin kasa a yankunan da abin ya shafa.

Source: Original
Karanta wasu labaran kan jihar Kebbi
- Ana maganar 2027, Gwamnan Kebbi ya kirkiro sabuwar masarauta a jiharsa
- Lokaci ya yi: Tsohon mataimakin gwamnan Kebbi ya rasu
- Bayan mako 1, 'yan bindiga sun dauki sabon mataki kan alkalin Kebbi da suka sace
Gwamnan Kebbi zai ci gaba da auren gata
A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan Jihar Kebbi, Dr Nasir Idris, ya jaddada aniyarsa ta ci gaba da gudanar da shirin auren gata na shekara-shekara domin tallafa wa marasa galihu a faɗin jihar.
Gwamna Nasir Idris ya bayyana hakan ne yayin bikin ɗaura auren ma'aurata 300 da aka gudanar a filin wasa na Haliru Abdu da ke Birnin Kebbi.
Dr Nasir Idris ya ce zai ƙara ƙaimi wajen tabbatar da cewa mutane masu ƙaramin ƙarfi suna ci gaba da cin gajiyar wannan shiri.
Asali: Legit.ng

