Fitaccen Mawaki Ya Ɗauki Abubuwan da ke Faruwa a Najeriya Ya Kai Gaban Shugaban Amurka
- Fitaccen mawakin Najeriya, Davido ya rubuta wasika ya sika wa Shugaban Amurka Donald Trump kan zaben gwamnan jihar Osun
- Mawakin ya nuna damuwa kan yiwuwar samun gagarumin tashin hankali da katsalandan a tsarin zaɓen
- Ya ce al’ummar jihar Osun na da haƙƙin a barsu du yi zaɓe cikin ’yanci, zaman lafiya da tsaro
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Osun - Fitaccen mawakin Najeriya, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya roƙi Shugaban Amurka Donald Trump da ƙasashen duniya su sa ido sosai kan zaɓen gwamnan jihar Osun da za a gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026.
Mawakin ya bayyana damuwarsa kan yiwuwar tashin hankali, tsoratar da masu zaɓe da kuma katsalandan ga tsarin dimokuraɗiyya yayin da siyasa ke ƙara zafi a jihar gabanin zaɓen.

Source: Instagram
Davido ya yi wannan kira ne a wata wasika da ya tura wa Shugaba Trump, da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata, 11 ga watan Agusta, 2027. inda ya yi magana kai tsayekan halin da ake ciki a Osun.
Davido ya nemi a kare masu zaɓe
A cikin saƙon, Davido ya ce akwai ƙarin damuwa game da tashe-tashen hankula da ka iya faruwa yayin zaɓen, musamman saboda zafin da siyasar jihar ta shiga.
Ya ce al’ummar Osun na da cikakken haƙƙin yin amfani da ikon da kundin tsarin mulkin Najeriya ya ba su na zaɓar shugabanninsu cikin ’yanci ba tare da tsoro ko tsoratarwa ba.
Mawakin ya ce:
“Ba ma son zubar da jini, ba ma son tsoratarwa, muna son zaman lafiya, gaskiya da kuma zaɓe na gaskiya da adalci.”
Davido ya kuma roƙi Shugaba Trump da sauran masu ruwa da tsaki na ƙasa da ƙasa da su sa ido kan yadda za a gudanar da zaɓen domin tabbatar da cewa an kare masu zaɓe tare da mutunta ƙuri’unsu.
Ya nuna damuwa kan tashin hankali
Kiran mawakin na zuwa ne a lokacin da abubuwa ke ƙara zafi a Osun yayin da jam’iyyun siyasa da ’yan takara ke shirin babban zaɓen da zai tantance wanda zai jagoranci jihar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa.

Kara karanta wannan
Zaben Osun: Saura kwana 5 a fara kada kuri'a, an bankado makarkashiyar da ake kullawa
Davido ya kasance yana magana a kai a kai kan abubuwan da suka shafi zaɓen Osun, wanda ya jawo hankalin jama’a saboda fafatawar da ake yi tsakanin gwamnan jihar mai ci, Ademola Adeleke, da sauran manyan ’yan takara.
Gwamna Adeleke kuma kawun Davido ne, lamarin da ya sa mawakin ke da alaƙa ta musamman da siyasar jihar, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

Source: Getty Images
Abin da Davido yake bukata
Davido ya jaddada cewa babban abin da ya kamata a mayar da hankali a kai shi ne tabbatar da cewa mazauna Osun sun je rumfunan zaɓe cikin kwanciyar hankali, ba tare da an tsoratar da su ko tilasta musu zaɓen wani ɗan takara ba.
Ya kuma yi kira ga hukumomin da ke da alhakin tsaron zaɓe da gudanar da shi da su tabbatar da cewa an kare masu zaɓe kuma babu wani abu da zai kawo cikas ga tsarin dimokuraɗiyya.
Mawakin ya ce sa ido daga ƙasashen duniya na iya taimakawa wajen ƙara tabbatar da cewa an gudanar da zaɓen cikin gaskiya da adalci.
Osun 2026: an kama kwamishinan Adeleke
An ji cewa rundunar ’yan sandan Osun ta kama Mayowa Adejoorin, kwamishinan muhalli da tsaftar muhalli na jihar kan harbe harben da aka yi a taron APC.
Kamen dai ya janyo martani daga Imole Campaign Council, kungiyar yakin neman zaben Gwamna Ademola Adeleke , wadda ta zargi ’yan sanda da nuna son kai.
Asali: Legit.ng
