Sokoto: Sunayen Malamai da Za Su Tantance Kalaman Sheikh Musa Lukuwa kan Annabi SAW

Sokoto: Sunayen Malamai da Za Su Tantance Kalaman Sheikh Musa Lukuwa kan Annabi SAW

  • Gwamnan Sokoto, Ahmed Aliyu ya kafa kwamitin mutum 14 domin bincike kan kalaman da aka yi kan iyayen Annabi Muhammad SAW
  • Kwamitin zai binciki batutuwan da Sheikh Musa Lukuwa ya gabatar da kuma tasirinsu ta fuskar Shari’a da addini
  • Kwamitin ya kunshi manyan malamai, masana shari’a, jami’an gwamnati da wakilan kungiyoyi da darikun Musulunci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya kafa kwamiti mai mutum 14 domin binciken kan kalaman da wasu malaman musulunci suka yi da wasu ke ganin batanci ne ga Annabi SAW.

Mai magana da yawun gwamnan, Abubakar Bawa, ne ya bayyana kafa kwamitin a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Gwamnan Sakkwato.
Gwamnan jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu a fadar gwamnatinsa Hoto: Ahmed Aliyu Sokoto
Source: Twitter

Premium Times ta ce kwamitin da Yahaya Boyi ke jagoranta zai duba tasirin batutuwan da Sheikh Musa Lukuwa ya gabatar ta fuskar doka da addini, wadanda ake zargin sun yi rashin mutunci ga akidar wasu.

Kara karanta wannan

Murtala Asada ya caccaki gwamnatin Sokoto kan rufe masallacin Sheikh Lukuwa

An kafa kwamitin ne sakamakon damuwa da aka nuna kan wasu kalamai da aka yi a bainar jama’a wadanda suka kara ta’azzara zaman dar-dar na addini a fadin jihar.

Daya daga cikin kalaman da suka tunzura jama'a akwai batun makomar iyayen Annabi Muhammad SAW, wadanda wasu suka nuna bacin ransu.

Abin da kwamitin zai bincika

Daga cikin abubuwan da aka dora wa kwamitin akwai yin nazari mai zurfi kan matsayin Shari’a game da batutuwan da Sheikh Lukuwa ya gabatar tare da bai wa gwamnatin jihar shawarar matakin da ya dace ta dauka.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa da shawarwarinsa ga gwamnatin jihar Sokoto cikin kwanaki 14.

Kwamitin ya kunshi manyan malamai, masana harkokin shari’a, manyan jami’an gwamnati da wakilan manyan kungiyoyi da darikun Musulunci daga ciki da wajen jihar ta Sokoto da ke Arewa maso Yamma.

Sunayen mambobin kwamitin

Malaman da gwamnatin Sakkwato ta zakulo ta sanya a cikin wannan kwamiti sun hada da:

Kara karanta wannan

Ana cikin wahala a ƙasa, Atiku, Tinubu sun kwashi miliyoyin dala sun kashe a Amurka

Yahaya na Malam Boyi (Sarkin Malamai) – Shugaba

Muhammad Isah Mafara – Mamba

Bello na Malam Boyi – Mamba

Mansur Ibrahim, mni – Mamba

Mansur Ibrahim Sa’id – Mamba

Wakilin Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatas Sunnah (Izala) ta Kaduna – Mamba

Wakilin Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatas Sunnah (Izala) ta Jos – Mamba

Wakilin Kungiyar Darikar Tijjaniyyah – Mamba

Wakilin Kungiyar Darikar Qadiriyyah – Mamba

Wakilin Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) – Mamba

Wakilin Majalisar Masarautar Sarkin Musulmi ta Sokoto – Mamba

Kwamishinan Addini na jihar Sakkwato – Mamba

Lawal Maidoki – Mamba

Barr. Gandi Umar Muhammad, mni – Sakatare

Lukuwa.
Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sakkwato da Sheikh Musa Lukuwa a gefen hagu Hoto: Ahmed Aliyu Sokoto
Source: Facebook

An rufe masallacin Sheikh Musa Lukuwa

A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin jihar Sokoto ta bayar da umarnin rufe Masallacin Juma’a na Sheikh Musa Lukuwa da ke Mabera bayan harin da ya yi sanadin kisa.

Kara karanta wannan

Uba Sani ya dauko hanyar gyara, ya nada kwamishinoni 3 da hadimai 45

Gwamnati ta bayyana masallacin a matsayin wurin da aka aikata laifi zai ci gaba da kasancewa a rufe har sai an ba da wani sabon umarni.

Ta kuma nisanta kanta daga duk wani mutum, ba tare da la’akari da matsayinsa ba, da ke fakewa da addini domin zagon kasa ko nuna rashin girmamawa ga Annabi Muhammad (SAW), iyayensa, iyalansa da sahabbansa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262