Ana Wata Ga Wata: Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano Ya Yi Murabus

Ana Wata Ga Wata: Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano Ya Yi Murabus

  • Shugaban Hukumar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Saidu Yahaya, ya yi murabus daga muƙaminsa
  • Yahaya ya miƙa takardar murabus ɗinsa ranar Talata yayin da ake fuskantar matsin lamba daga gwamnatin Kano kan yadda yake gudanar da ayyukansa
  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Barista Hafsat Ada’u Kutama a matsayin shugabar riƙon kwarya ta hukumar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Shugaban Hukumar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Saidu Yahaya, ya yi murabus daga muƙaminsa.

Saidu Yahaya ya miƙa takardar murabus ɗinsa a jiya Talata, bayan matsin lambar da ake zargin ya fuskanta daga gwamnatin Jihar Kano saboda rashin cika abubuwan da ake sa ran zai yi wajen gudanar da ayyukansa.

Saidu Yahaya.
Tsohon shugaban hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Saidu Yahaya Hoto: Yahaya Shehu
Source: Facebook

Ko da yake ba a sanar da murabus ɗin a hukumance ba, Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta nuna cewa an riga an naɗa sabon shugabanci a hukumar.

Kara karanta wannan

Sanata Yari na jagorantar kamfen din Tinubu, ya yi babban rashi a rayuwa

Gwamna Abba ya nada shugabar PCACC

Mai ba Gwamna Abba Kabir Yusuf shawara kan kafafen sada zumunta, Ibrahim Adam, ya sanar a shafinsa na Facebook cewa gwamnan ya naɗa Barista Hafsat Ada’u Kutama a matsayin shugabar riƙon kwarya ta PCACC.

“Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Bar. Hafsat Ada’u Kutama a matsayin Shugabar Riƙon Kwarya ta Hukumar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (PCACC) ta Jihar Kano.
“Har zuwa lokacin naɗa ta, Barista Hafsat ta kasance sakatariyar hukumar,” in ji shi.

Ana sa ran Kutama za ta fara aiki a matsayin shugabar riƙon kwarya daga yau, Laraba, 16 ga watan Satumba, 2026.

Lokacin da aka naɗa Saidu Yahaya

An naɗa Saidu Yahaya a matsayin shugaban hukumar a watan Agustan 2025, bayan wa’adin tsohon shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya ƙare.

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da naɗin nasa na wa’adin shekaru biyar.

Kara karanta wannan

'Yan gwagwarmaya sun kaddamar da tafiyar kifar da Tinubu a 2027

Wannan ci gaba ya zo ne bayan sukar da Gwamna Abba ya yi a baya-bayan nan kan yadda hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ke gudanar da ayyukanta ƙarƙashin jagorancin Yahaya.

Abba.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yana jawabi a wurin taron magoya baya Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Gwamnan ya taɓa ƙalubalantar shugaban hukumar a bainar jama’a da ya ƙara kaimi wajen yaƙi da cin hanci da rashawa, yana mai gargaɗin cewa duk wanda ba ya son sauke nauyin da aka ɗora masa ya kamata ya “sauka”.

Gwamna Abba ya yi karin albashi a Kano

Kun ji cewa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya waiwayi wasu daga cikin jami'o'in da ke jihar da karin albashi inda aka fitar masu da sabon tsari.

Ma'aikatan da aka bullo wa da wannan tsari sun hada da na Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil da Jami’ar Northwest da ke Kano.

Gwamnatin jihar za ta kashe sama da N391m duk wata wajen biyan sabon tsarin albashin ma’aikatan jami’o’in biyu saboda inganta rayuwarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262