Tsohon IGP Ya Fallasa Gwamnati, Ya Fadi abin da Ya Jawo Lalacewar Tsaron Najeriya
- Tsohon sufeta janar na 'yan sanda ya ce gwamnatin tarayya ta raunana ‘yan sanda da gangan ta hanyar kin samar musu da isassun kayan aiki
- Mike Okiro ya ce rashin ɗaukar sababbin jami’ai na tsawon shekaru biyar ya rage ƙarfin rundunar bayan dubban jami’ai sun bar aiki
- Tsohon IGP ya buƙaci hukumomin tsaro su riƙa musayar bayanan sirri kai tsaye domin dakile hare-haren masu aikata laifuka cikin gaggawa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Abuja - Tsohon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mike Okiro (mai ritaya), ya zargi gwamnatin tarayya da gangan da raunana rundunar ‘yan sanda ta Najeriya ta hanyar rashin samar mata da isassun makamai da kayan aiki, yana cewa hakan ya ƙara ta’azzarar matsalar tsaro a ƙasar.
Okiro ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin taron tattaunawa kan tsaro da aka gudanar a Abuja.

Source: Facebook
An zargi gwamnati kan rashin tsaro
A yayin taron, Okiro ya ce rundunar ‘yan sanda ita ce babbar hukuma da ke kula da tsaron cikin gida, amma gwamnati ta gaza ba ta goyon bayan da ya dace, in ji rahoton Punch.
Ya ce:
“Gwamnati tana ba da gudummawa wajen matsalar tsaro. Rundunar ‘yan sanda ita ce ke jagorantar tsaron cikin gida, amma gwamnati ta raunana ta da gangan. Sakamakon haka shi ne matsalar rashin tsaro.”
Tsohon shugaban rundunar ya ce yanayin tsaro ya sauya, don haka ba zai yiwu jami’in ‘yan sanda ya ci gaba da aiki da tsoffin kayan aiki ba.
“Mun wuce lokacin da ɗan sanda zai riƙa sintiri da sanda kawai. Gwamnati ta samar wa hukumomin tsaro makamai, motocin sulke, na’urorin sadarwa da sauran kayan aikin zamani domin su iya gudanar da aikinsu yadda ya kamata,” in ji shi.
Tsohon IGP ya yi korafi kan daukar jami’ai
Okiro ya kuma danganta ƙarancin jami’an ‘yan sanda da rashin ɗaukar sababbin ma’aikata tsawon shekaru.
Ya tuna cewa lokacin da yake shugaban hukumar da ke kula da 'yan sanda (PSC) a shekarar 2013, sun gano cewa ba a ɗauki sababbin 'yan sanda ba na tsawon shekaru biyar duk da cewa jami’ai da dama sun yi ritaya, sun rasu ko suka bar aiki.
Ya ce:
“A lokacin mun gano cewa rundunar ta rasa jami’ai 59,730 ba tare da maye gurbinsu ba. A lokaci guda kuma akwai dubban matasa masu ilimi da ba su da aikin yi."

Source: Twitter
Bukar hadin kan hukumomi
Okiro ya kuma soki yadda hukumomin tsaro ke tafiyar hawainiya wajen musayar bayanan sirri.
Ya ce lokacin yana Sufeto Janar ya taba rubuta wa Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro cewa jami’an tsaro su riƙa musayar bayanai kai tsaye maimakon jiran amincewa daga hedikwata.
Ya ce irin wannan haɗin gwiwa zai taimaka wajen dakile hare-haren masu aikata laifuka cikin gaggawa da kuma inganta tsaron ƙasa.
Dalilin karfin Boko Haram a Najeriya
Tun da fari, mun ruwaito cewa, tsohon IGP Mike Okiro ya ce rushe rundunar ATS da ya kafa ne ya ba Boko Haram damar samun ƙarfi da bazuwa a Najeriya.
Mike Okiro ya bayyana cewa ya horas da jami'an ATS a ƙasashen waje tare da kafa cibiyar horaswa a Ribas domin yaƙi da ta'addanci.
Tsohon sufeta janar din ya yi zargin cewa rashin goyon bayan gwamnati da dakatar da shirin ne ya raunana matakan dakile Boko Haram tun daga farko.
Asali: Legit.ng


