Ana Shirin Zaɓen 2027, Gwamna Ya Nemi Afuwar Ƴan Ƙabilar Igbo kan Yaƙin Basasa
- Ana shirin zaben shekarar 2027, Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya nemi afuwar al'ummar Igbo baki daya
- Mutfwang ya yabawa Igbo saboda gudunmawar tattalin arziki, ya bukace su su ci gaba da hada kai, su zuba jari tare da horas da matasan Plateau
- Shugabannin al'ummar Igbo sun amince da Mutfwang a matsayin dan takararsu na gwamna a shekarar 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Jos, Plateau - Gwamnan Plateau, Caleb Mutfwang, ya nemi afuwar al'ummar Igbo kan yakin basasa da aka yi.
Mutfwang ya fadi haka ne bayan rawar da jihar ta taka a yakin basasar Najeriya, yana mai cewa an yaudari mutanen Filato suka shiga yakin.

Source: Twitter
Hakan na cikin wani jawabinsa a taron tattaunawa da shugabannin al'ummar Igbo daga kananan hukumomi 17 na Plateau, cewar Punch.
Mutfwang ya bukaci a birne abubuwan da suka faru a baya inda ya ce tuna su zai sake dawo da abubuwa baya.
Gwamnan ya yabawa al'ummar Igbo kan irin gudunmawar da suke bayarwa wajen bunkasa tattalin arzikin Plateau, yana mai cewa suna daga cikin ginshikan ci gaban jihar.
Ya ce tun bayan kare yakin basasa, Plateau, ta kasance daya daga cikin jihohin da suka fi karbar al'ummar Igbo hannu bibbiyu, yana mai tunatar da cewa an biya wasu diyya saboda asarar da suka yi.
Mutfwang ya ce:
"Ina neman afuwar al'ummar Igbo domin mu bar abin da ya faru a baya, mu ci gaba da karfafa hadin kai. Mun zama iyali guda saboda an yaudari mutanenmu suka shiga yaki, kuma muna nadamar hakan. Dole mu rufe wannan shafi mu ci gaba.
"Dole mu hada kai. Muna son al'ummar Igbo su dauke mu a matsayin 'yan'uwa, tare mu samar da yanayin da kowa zai samu damar cigaba."
Gwamnan ya kuma roki 'yan kasuwar Igbo da ke Plateau su tallafa wa 'yan asalin jihar ta hanyar samar da ayyukan yi, horaswa da zuba jari domin matasa.
"Najeriya kasa ce mai girma, kuma babu wata kabila da ta nuna hazakar kasuwanci fiye da Igbo. Ina rokon ku ku yada wannan ruhin a Plateau, sannan ku dauki matasan Plateau aiki ku kuma horas da su."
- Caleb Mutfwang
A yayin taron, shugabannin al'ummar Igbo sun bayyana goyon bayansu ga Mutfwang domin ya sake tsayawa takarar gwamna a zaben 2027 saboda shugabancinsa mai hada kan jama'a da gudanar da mulki cikin adalci.
Shugaban al'ummar Igbo a Plateau, Cif Chidi Onah, ya sanar da amincewar, yana cewa gwamnan ya nuna kwarewa, gaskiya da jajircewa wajen tabbatar da daidaito da ci gaba.
Ya ce:
"Mun amince da Gwamna Caleb Mutfwang a matsayin dan takarar da al'ummar Igbo za su mara wa baya a zaben gwamna na 2027. "Mun yi hakan ne saboda kwarewarsa, mutuncinsa da shugabanci nagari."
Onah ya kara da cewa gwamnan ya inganta zaman lafiya, ya samar da yanayin da kasuwanci ke bunkasa, sannan ya tsaya tare da al'ummar Igbo lokacin rasuwar sarkinsu.
Ya kuma yabawa kokarin gwamnan wajen ci gaban Filato, yana cewa jihar ta zama wuri mafi dacewa da kasuwanci da zuba jari, cewar The Guardian.
Ya ce al'ummar Igbo sun zauna a Plateau tun kafin samun 'yancin kan Najeriya, yana mai godewa gwamnan saboda biyan diyya ga wasu daga cikinsu kan rikicin kadarori.
Tsohon shugaban al'ummar Igbo a Plateau, Mike Okunonke, ya ce Igbo mutane ne masu son zaman lafiya kuma suna taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tattalin arzikin jihar.
Ya bayyana cewa goyon bayansu ga Mutfwang ya samo asali ne daga irin ayyukan da ya gudanar, ba wai saboda jam'iyyarsa ba.
Meta description:
Asali: Legit.ng


