Bodejo: Kotu Ta Yi Hukunci kan Bukatar Neman Belin Shugaban Miyetti Allah

Bodejo: Kotu Ta Yi Hukunci kan Bukatar Neman Belin Shugaban Miyetti Allah

  • Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da belin Shugaban Miyetti Allah, ​Bello Bodejo, kan kudi N2bn
  • Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Bello Bodejo da safarar kudin haram da ya kai dala miliyan 2.63
  • Babbar Kotun ta bukaci mai tsaya masa ya kasance mazaunin Abuja kuma ya mallaki kadarar da ta kai N2bn

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da belin Shugaban Miyetti Allah, Bello Bodejo, kan kudi N2bn.

An bayar da belin ne a ranar Litinin, 20 ga watan Yulin 2026 yayin da ake ci gaba da shari’ar da ake tuhumarsa da safarar kudin haram da ya kai dala miliyan 2.63.

Bodejo ya samu beli a wajen kotu
Shugaban kungiyar Miyetti Allah, Bello Bodejo Hoto: Alhaji Bello Bodejo
Source: Facebook

Jaridar The Punch ta kawo rahoton cewa Mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da belin ne bayan ya yanqqqqke hukunci kan bukatar Bodejo.

Kara karanta wannan

Hotunan jami'a, gidan rediyo da sauran kadarori 46 da aka kwace a hannun Malami

Kotu ta bayar da belin Bello Bodejo

Mai shari'a Inyang Ekwo ya ce laifuffukan da ake tuhumarsa da su na da damar beli, kuma kotun tana da ikon bayar da belin.

Alkalin ya umarci wanda zai tsaya wa wanda ake tuhuma da ya kasance da kudin da ya yi daidai da adadin belin, wato N2bn.

Ya ce dole ne mai tsaya masa ya kasance mazaunin Abuja kuma yana da takardar shaidar biyan haraji ta tsawon shekaru uku.

Justice Ekwo ya kuma umarci mai tsaya masa ya mallaki kadarar fili da ta kai darajar N2bn a Abuja. Ya kara da cewa magatakardar kotun zai tantance takardun mallakar kadarar.

Kotun ta hana Bodejo tafiya

Alkalin ya kuma umarci Bodejo da ya mika fasfo dinsa na kasa da kasa ga magatakardar kotun, tare da hana shi fita daga Najeriya ba tare da izinin kotun ba.

Hakazalika ya dage shari’ar zuwa ranakun 5, 6 da 7 ga Oktoba 2026 domin fara sauraron karar.

Kara karanta wannan

Akpabio ya kare dangantakar majalisa da Tinubu, ya fadi dalili

EFCC ta tuhumi Bodejo

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Laifukan Tattalin Arziki (EFCC) ta gurfanar da Bodejo a ranar 9 ga Yuli kan tuhume-tuhume da dama da suka shafi zargin safarar kudin haram da ya kai kusan dala miliyan 2.63.

Shugaban na kungiyar Miyetti Allah ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da hukumar EFCC yi masa, jaridar Vanguard ta kawo rahoton.

Bayan gurfanar da shi, lauyan masu gabatar da kara, Wahab Shittu (SAN), ya nemi a sanya ranar fara shari’a tare da rokon kotu ta tsare wanda ake tuhuma a hannun EFCC.

Bello Bodejo ya samu beli
Bello Bodejo zaune yayin zaman kotu Hoto: @OfficialEFCC
Source: Twitter

Sai dai lauyan Bodejo, Ahmed Raji (SAN), ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar beli mai dauke da kwanan wata 30 ga Yunin 2026.

Raji ya ce laifukan da ake zargin wanda yake karewa da su na da damar beli karkashin dokar, sannan ya bukaci kotu ta amince da bukatar.

Sai dai, lauyan hukumar EFCC, Wahab Shittu ya yi adawa da bukatar, inda ya roki kotu ta ki bayar da belin.

Kara karanta wannan

Bayan umarnin kotu, an kama shugaban hukumar bogi da ake ta cece kuce a kanta a Najeriya

Miyetti Allah ta nemi a saki Bodejo

A wani labarin kuma, kun ji cewa kungiyar Miyetti Allah Miyetti Allah ta yi kira da a saki shugabanta na kasa, Alhaji Bello Bodejo da aka cafke.

Kungiyar Miyetti Allah ta bukaci shugabannin da ke kula da shari'ar da su tabbatar an yi wa shugabansu adalci kasancewar shi ma dan Najeriya ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng