'Yan Bindiga Sun Shiga Uku, Tinubu Ya Shirya Amfani da Fasahohin Zamani a Najeriya

'Yan Bindiga Sun Shiga Uku, Tinubu Ya Shirya Amfani da Fasahohin Zamani a Najeriya

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ƙara kaimi wajen amfani da sababbin fasahohi wajen yaƙi da rashin tsaro
  • Tinubu ya bayyana cewa ana zuba jari wajen sayen kayan aikin sojoji na zamani da horas da jami'ai domin murkushe duk wata barazana
  • Gwamnan jihar Ribas karkashin jagorancin Gwamna Siminalayi Fubara da Hafsan Sojin Ƙasa sun yabawa jami'an soji kan ƙoƙarinsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers, Nigeria - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na magance matsalar tsaro ta hanyar amfani da sababbin fasahohi na zamani.

Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta yi amfani da fasahohin zamani, ayyukan tattara bayanan sirri da kuma ci gaba da inganta rundunar sojojin Najeriya domin dawo da zaman lafiya.

Shugaba Tinubu.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana magana a wurin taro a Abuja Hoto: @OfficialABAT
Source: Facebook

Daily Trust ta rahoto cewa Bola Tinubu ya bayyana hakan ne a jiya Litinin yayin rufe bikin ranar Sojojin Najeriya ta 2026 da kuma taron African Land Forces Forum (ALFF) da aka gudanar a Fatakwal, jihar Ribas.

Kara karanta wannan

Aisha Buhari: 'Manyan abubuwa 2 da tsohon shugaban ƙasa ya bari a Najeriya'

Mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ne ya wakilci shugaban ƙasar a wajen taron.

Gwamnatin Tinubu na ƙarfafa rundunar soji

A cewarsa, gwamnatinsa na ci gaba da zuba jari wajen samar da kayan aikin soja na zamani da kuma horas da dakarun domin inganta shirye-shiryen yaƙi da ƙara ƙarfafa shirinsu na fuskantar barazanar tsaro.

Ya ce:

"Gwamnatina ta himmatu wajen yaƙar sababbin barazanar tsaro ta hanyar amfani da fasahohi na zamani da kuma ƙarfafa ƙwarewar jami'anmu a dukkan fannonin aiki."

Njeriya za ta ƙara ƙera kayan aikin soja

Tinubu ya kuma jaddada muhimmancin bincike, ƙirƙire-ƙirƙire da samar da kayan aikin sojoji a cikin gida, kamar yadda tashar Channels tv ta ruwaito.

Ya bayyana cewa farfaɗo da masana'antar kera makaman sojoj (DICON) na da nufin bai wa Najeriya damar ƙera kayan aikin tsaro da kanta tare da rage dogaro da ƙasashen waje.

Shugaban ya bayyana taron African Land Forces Forum a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen Afirka, bunƙasa diflomasiyyar tsaro da kuma musayar ilimi da ƙwarewa.

Kara karanta wannan

Murkushe ƴan adawa da abu 3 da ƴan Najeriya ke fargaba game da ƴansandan jihohi

Zaman lafiya ya dawo Ribas

Tun da farko, gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce karɓar baƙuncin taron ya nuna cewa zaman lafiya da kwanciyar hankali sun dawo jihar.

Gwamnan ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya ta ƙara kula da walwalar jami'an rundunar sojoji.

Sojoji.
Dakarun rundunar sojin Najeriya a bakin aiki Hoto: @NigerianArmy
Source: Twitter

Shi ma Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya sake tabbatar da aniyar rundunar sojojin Najeriya na kare yankunan ƙasar da rayuka da dukiyoyin al'umma duk da sauye-sauyen barazanar tsaro.

Tinubu na zuba ayyuka a Arewa

A wani labarin, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa yankin Arewa ta Tsakiya na da matukar muhimmanci ga gwamnatinsa.

Mai giram Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na kan gudanar da ayyukan tituna 61 a wannan yaki kuma ana sa ran za su inganta rayuwar al'umma.

A cewarsa, jihohin yankin ba su taba cin gajiyar irin wannan gagarumin shirin raya ababen more rayuwa daga gwamnatin tarayya kamar yadda ake yi yanzu ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262