"Ba Yan Bindiga ba ne," Rundunar 'Yan Sanda Ta Fadi Wadanda Aka Gani Dauke da Makamai a Bidiyo

"Ba Yan Bindiga ba ne," Rundunar 'Yan Sanda Ta Fadi Wadanda Aka Gani Dauke da Makamai a Bidiyo

  • Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta karyata zargin cewa jami’anta suna mu’amala da ‘yan bindiga a jihar Katsina
  • Hakan na zuwa ne bayan wani bidiyon da ya karade kafafen sada zumunta ya nuna ‘yan sanda suna gaisawa da wasu dauke da makamai a kan babura
  • ‘Yan sanda sun ce mutanen da ke cikin bidiyon ba ‘yan bindiga ba ne, mambobin kungiyar sintiri ta bijilanti (VGN) ne da mafarauta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Rundunar ‘yan sandan Najeriya (NPF) ta karyata rahotannin da ke yawo cewa wasu jami’anta suna mu’amala ko hada kai da ‘yan bindiga a jihar Katsina.

Zargin ya samo asali ne daga wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, wanda ya nuna wasu jami’an ‘yan sanda suna gaisawa da wasu dauke da makamai a kan babura.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta yi maganar da ta ba da mamaki kan tsaro

Yan sanda.
Sufetan yan sandan Najeriya, Tunji Disu da bidiyon yadda yan bijilanti suka wuce ga gefan jami'ai a Katsina Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

A bidiyon wanda tsohon sanatan Daura, Ahmad Babba Kaita ya wallafa a Facebook, an ga 'yan sanda sun kauce sun bar mutanen da ake zargin yan bindiga ne na wucewa a kan babura.

Rundunar 'yan sanda ta yi bayani

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Anietie Iniedu, ya fitar ranar Laraba, ya bayyana cewa mutanen da aka gani a bidiyon ba ‘yan bindiga ba ne.

A cewarsa, su mambobi ne na kungiyar 'yan bijilanti (VGN) da kuma mafarauta da aka yi wa rajista, wadanda ke taimakawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyuka a yankunan Musawa da Matazu na jihar Katsina.

A sanarwar da rundunar 'yan sandan ta wallafa a shafin X, ta ce:

“Bidiyon ya nuna abin da aka saba tsakanin yan sanda da yan bijilanti, wadanda ke taimakawa harkokin tsaro yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa wurin aiki domin tallafawa yaki da miyagu da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Kara karanta wannan

Rundunar yan sanda ta haramta wa jami'anta tin Facebook, TikTok

Yan sanda sun ce zargin karya ne

Iniedu ya jaddada cewa duk wani zargi da ke cewa jami’an ‘yan sanda suna hulda da ‘yan bindiga karya ne kuma an yi shi ne domin yaudarar jama’a.

Ya ce yaɗa irin wadannan bayanai na iya haifar da fargaba, rage amincewar jama’a da hukumomin tsaro da kuma kawo cikas ga ayyukan tsaro da ake gudanarwa.

Yan sanda.
Jami'an rundunar yan sanda ta Najeriya a bakin aiki Hoto: @PoliceNG
Source: Getty Images

An gargadi masu yada labaran karya

Rundunar yan sanda ta bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da rahotannin da ke da alaka da bidiyon tare da rika dogaro da bayanan da hukumomin tsaro ke fitarwa a hukumance.

Ta kuma gargadi mutane ko kungiyoyin da ke kirkira ko yada labaran karya da ka iya barazana ga zaman lafiya da tsaro da cewa za a iya daukar matakin doka a kansu.

An hana yan sanda amfani da TikTok

A wani labarin, kun ji cewa Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Olatunji Disu, ya haramta wa jami’an ‘yan sanda amfani da kafafen sada zumunta a Najeriya.

Kara karanta wannan

Bayan mutuwar jigo a Izala, tsohon shugaban APC ya rasu a hannun yan bindiga

Dokar ta hana jami’ai dauka ko wallafa bidiyo, hotuna, barkwanci ko shirye-shirye kai tsaye cikin kayan ‘yan sanda ba tare da izini ba.

Dokar ta kuma hana jami’an yin sharhi a bainar jama’a kan binciken ‘yan sanda, ladabtarwa, sauya wurin aiki ko wasu harkokin hukuma.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262