Rashin Tsaro: Gwamna Radda Ya Sanya Labule da Sarakunan Gargajiya a Katsina
- Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya gudanar da wani taro tare da manyan sarakunan gargajiya kan matsalar rashin tsaro
- Taron ya hada da sarakunan Katsina da Daura tare da Hakimai da Dagatai daga sassa daban-daban na jihar domin tattauna muhimman batutuwa
- Gwamna Radda ya nuna muhimmancin da sarakunan gargajiya suke da shi wajen tabbatar da dorewar zaman lafiya a cikin al'umma
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya gana da sarakunan gargajiya kan matsalar rashin tsaro.
Gwamna Radda ya jaddada muhimmancin sarakunan gargajiya wajen haɓaka zaman lafiya, tsaro, da kuma ci gaban al'ummomin mazauna karkara a faɗin jihar.

Source: Facebook
Gwamna Radda ya bayyana hakan ne yayin wani taron da ya yi da sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, 18 ga watan Yunin 2026, kamar yadda sakataren yada labaransa, Ibrahima Kaulaha Mohammed ya sanya a shafinsa na Facebook.
Gwamna Radda ya gana da sarakunan gargajiya
Taron ya gudana tsakaninsa da Mai Martaba Sarkin Katsina, HRH Abdulmumini Usman; da Mai Martaba Sarkin Daura, HRH Umar Farouq Umar; tare da haɗin gwiwar Hakimai da Dagatai daga sassa daban-daban na jihar.
Taron wanda aka gudanar zauren taro na Ggdan gwamnati da ke Katsina, yana daga cikin ƙoƙarin da gwamnatin ke yi na zurfafa alaƙa da shugabannin gargajiya tare da ƙarfafa matakan da suka ginu a kan al'umma domin gudanar da mulki, tsaro, da kuma ci gaba mai dorewa a faɗin jihar Katsina.
A kan me Radda da sarakuna suka tattauna?
Ganawar ta fi mayar da hankali ne a kan muhimman batutuwan da suka shafi shugabanci, ci gaban al'umma, da kuma tsaro, tare da ba da fifiko na musamman wajen ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da sarakunan gargajiya.
Gwamna Radda ya lura cewa sarakunan gargajiya sun kasance abokan haɗin gwiwa masu mahimmanci wajen dorewar zaman lafiya, haɓaka haɗin kai, da kuma tallafa wa manufofi da shirye-shiryen gwamnati a matakin karkara.
Ya jaddada buƙatar ci gaba da haɗin gwiwa domin tunkarar ƙalubalen tsaro da kuma hanzarta kawo ci gaba a cikin al'ummomi daban-daban.

Source: Facebook
Manyan jami'an gwamnati sun halarci taron
Taron ya haɗa manyan jami'an gwamnati, ciki har da Shugaban Majalisar dokokin jihar Katsina, Nasir Daura, babban alƙalin jihar Katsina, Musa Abubakar.
Sauran sun hada da shugaban ma'aikatan fadar gwamnati, Abdulkadir Nasir; sakatare na musamman ga gwamna, Abdullahi Turaji da sauran mambobin majalisar zartarwa ta jihar Katsina.
Yusuf Ahmad da ke zaune a Katsina, ya bayyana cewa yana da kyau a rika tattaunawa da iyayen kasa kan matsalar rashin tsaro.
"Sarakunan sune mutanen da ke tare da al'umma a koda yaushe. A ganina suna da rawar da za su taka wajen magance rashin tsaro."
"Muna rokon dai Allah ya kawo mana karshen wannan bala'in."
- Yusuf Ahmad
'Yan bindiga sun kashe dan kasuwa a Katsina
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga sun yi aika-aika a jihar Katsina ta hanyar hallaka wani fitaccen dan kasuwa kuma manomi, mai suna Bala Sanin Kawo.
Majiyoyi sun nuna cewa yan ta'addan sun kashe mutumin ne kwanaki kaɗan bayan sun yi garkuwa da shi a ƙaramar hukumar Dandume ta jihar Katsina.
Iyalan mamacin sun tattara kuɗin fansar da aka bukata tare da miƙa su kamar yadda masu garkuwar suka umarta, amma bayan an kai kuɗin sai maharan suka fadi wurin da suka ajiye gawarsa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


