CUPP Ta Goyi bayan Wasu Yan Majalisa da Suka ba Shugaba Tinubu Zabi 1 ko Ya Yi Murabus

CUPP Ta Goyi bayan Wasu Yan Majalisa da Suka ba Shugaba Tinubu Zabi 1 ko Ya Yi Murabus

  • Gamayyar jam'iyyun siyasa a Najeriya (CUPP) ta goyi bayan kiran da ƴan Majalisar Wakilai na tsagin adawa suka yi ga Shugaba Bola Tinubu
  • Kungiyar ta bayyana cewa kamata ya yi duk shugaban da ya kasa samar da ingantaccen shugabanci ya sauka daga mulki cikin mutunci
  • Ta bukaci gwamnatin tarayya ta dauki matakan gaggawa kan tsaro da matsin tattalin arziki domin shawo kan matsalolin kasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gamayyar jam'iyyun siyasa a Najeriya (CUPP) ta bayyana goyon bayanta ga kiran da ƴan Majalisar Wakilai na tsagin adawa suka yi ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ya dauki matakai ko ya yi murabus.

Mukaddashin Shugaban CUPP na kasa Cif Peter Ameh, ne ya bayyana matsayar kungiyar a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Kara karanta wannan

Mutuwar Janar Rabe: Kwankwaso ya kai ziyara Katsina, ya bada mafita kan matsalar tsaro

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Tinubu a fadar gwamnatin tarayya da ke Abuja Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Ya ce matsayar gamayyar jam’iyyun adawar ta yi daidai da ra’ayin ƴan majalisar wakilai na tsagin jam'iyyun adawa, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Tun farko, yan Majalisar wakilan sun bukaci Tinubu ya jagoranci kasar nan yadda ya kamata ta hanyar daukar matakan kare rayukan yan Najeriya ko kuma ya yi murabus.

CUPP ta bai wa Bola Tinubu zabi 2

Da take goyon bayan yan Majalisar, CUPP ta nuna cewa wajibi ne gwamnatin da ke mulki ta fuskanci kalubalen da ke addabar ƴan Najeriya ko kuma ta bai wa wasu damar jagoranci.

Ameh ya ce a kowace kasa mai mutunta tsarin dimokuradiyya, duk wani zababben shugaba da ya kasa samar da sakamakon da zai inganta rayuwar al’umma, ya kamata ya sauka daga mukaminsa cikin mutunci.

“Duk wani zababben jami’i da ya kasa samar da ingantaccen shugabanci da zai kyautata rayuwar jama’a ya kamata ya yi murabus cikin girmamawa,” in ji Ameh.

Kara karanta wannan

Matasan Arewa sun gano abin da ke kullawa domin sauke manyan hafsoshin tsaron Najeriya

Matakan da ake so Tinubu ya dauka

CUPP ta bukaci Tinubu da gwamnatinsa su dauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro, tsadar rayuwa da kuma halin kuncin tattalin arziki da ƴan Najeriya ke fuskanta.

A cewar kungiyar, shugabanci nauyi ne, ba gata ba, inda ta kara da cewa:

“Shugabanci ba hakki ba ne, nauyi ne. Idan ba a sauke wannan nauyi yadda ya kamata ba, hanya mafi dacewa ita ce yin murabus."
Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a gidan gwamnatin Najeriya Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Kungiyar ta sake tabbatar da kudirinta na ci gaba da fafutukar ganin an samar da nagartaccen shugabanci, gaskiya da rikon amana tare da kare muradun ƴan Najeriya.

Ta kuma bukaci shugaban kasa da ya saurari wannan kira tare da daukar matakai masu gamsarwa domin rage radadin halin da jama’a ke ciki a fadin kasar nan, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Wasu yan Majalisa sun taso Tinubu

A wani labarin, kun ji cewa yan majalisar wakilai na jam'iyyun adawa sun ba da shawara kan yadda ya kamata gwamnatin tarayya ta tunkari matsalolin Najeriya.

Kara karanta wannan

An bukaci Shugaba Tinubu ya ayyana wani shirin watanni 6 don magance matsalolin Najeriya

Sun bukaci shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ayyana wani shiri na watanni shida domin dawo da zaman lafiya da walwalar jama'a.

Yan majalisar ta bakin shugaban marasa rinjaye, Hon. Fred Agbedi, sun bukaci shugaba Tinubu ya dauki matakan da ya dace ko kuma ya yi murabus.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262