Wata Sabuwa: Ana Zargin Gwamnoni 6 na da Laifi a Batun Sace Daliban Oyo a Najeriya

Wata Sabuwa: Ana Zargin Gwamnoni 6 na da Laifi a Batun Sace Daliban Oyo a Najeriya

  • Batun sace dalibai da malaman wata makarantar sakandire a jihar Oyo na ci gaba da jawo martani daga daidaikun mutane da kungiyoyi
  • Kungiyar yarbawa ta AYDM ta zargi gwamnonin jihohin Kudu maso Yamma da yi wa harkar tsaro rikon sakainar kashi a yankin
  • AYDM ta yi ikirarin cewa gwamnonin suna da hannu da duk abubuwan da ke faruwa a yankin saboda gaza daukar matakan kariya tun farko

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Oyo, Nigeria - Ƙungiyar haɗin kan kabilar yarbawa ta AYDM ta zargi gwamnonin shiyyar Kudu maso Yamma da sakaci a harkar tsaro, wanda suka ce shi ya jawo sace dalibai a jihar Oyo.

Gwamnoni shida na Kudu maso Yamma dai sune Seyi Makinde (Oyo), Lucky Aiyedatiwa (Ondo), Biodun Oyebaniji (Ekiti), Dapo Abiodun (Ogun), Babajide Sanwo-Olu (Legas) da Ademola Adeleke (Osun).

Kara karanta wannan

Lokuta 3 da Babachir Lawal ya canza gidan siyasa daga mulkin Buhari zuwa yau

Gwamnonin Kudu.
Gwamnonin 6 na jihohin Kudu maso Yamma a wani taro da duka gudanar a jihar Oyo Hoto: Seyi Makinde
Source: Facebook

An fara zargin gwamnoni 6 a Kudu

A rahoton da The Cable ta wallafa, AYDM ta ce gwamnonin shida sun gaza ɗaukar matakan kariya da suka dace da suka shafi tsaro a yankin, duk da alamun kwararar 'yan ta'adda da suka gani.

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar AYDM, Popoola Ajayi ya fitar, ƙungiyar ta ce gwamnonin ba su yi wani yunkuri ba tun 2010, duk da ayyukan ta'addancin da ke faruwa a jihohin da ke makwabtaka da su a Arewa ta Tsakiya.

Haka kuma, ƙungiyar ta koka da cewa hukumar tsaro ta Kudu maso Yamma, Amotekun, wadda aka kafa domin magance rashin tsaro a yankin, ba ta da isassun kayan aiki kuma ba za ta iya yaƙar ta'addanci yadda ya kamata ba.

Sakacin da aka yi a Kudu maso Yamma

Sanarwar ta ce:

"Sun ga duk alamomin abin da ke shirin faruwa, amma ba su yi komai ba. Zuwa yanzu an kashe manyan sarakunan Yarabawa guda huɗu sakamakon hare-haren 'yan ta'adda.

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: Jam'iyyar APC ta bukaci Gwamna Seyi Makinde ya yi murabus

Kungiyar ta ba da misali da Oba Kehinde Falodun na Agamo da ke ƙaramar hukumar Akure ta Arewa a jihar Ondo, wanda aka kashe a cikin fadarsa ranar 18 ga Fabrairu, 2026 bayan ya ƙi yarda yunƙurin garkuwa da shi.

"Irin wannan ƙaddara ita ma ta faɗa wa Oba Adegoke Adewusi, Olufon na Ifon wanda 'yan fashi da makami suka harbe shi har lahira a ranar 26 ga Nuwamba, 2020, a kan titin Ifon-Benin da ke yankin Elegbeka," in ji ta.
Gwamna Makinde.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde yana magana a taron majalisar zartarwa Hoto: Seyi Makinde
Source: Twitter

Kungiyar AYDM ta kuma yi ikirarin cewa babu ɗaya daga cikin gwamnonin jihohin Kudu maso Yamma da ya ziyarci iyalai sarakunan gargajiyan domin yi mas jaje da ta'aziyya, in ji rahoton Vanguard.

Ƙungiyar ta ce sace ɗaliban makaranta da malamai daga ƙaramar hukumar Oriire a jihar Oyo ya tabbatar da "halin ko'in kula, sakaci da rashin nuna damuwa na shugabannina yankin."

Ana zargin Makinde kan sace daliban Oyo

A wani labarin, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya yi zargin cewa Gwamna Seyi Makinde ne ya kitsa sace dalibai a Oyo dok bata sunan Shugaba Bola Tinubu.

Ya ce Makinde bai mayar da martani ko daukar matakin gaggawa ba bayan sace daliban, yana zargin cewa ya fi mayar da hankali kan harkokin siyasa fiye da magance matsalar.

Kara karanta wannan

Adelabu: Tsohon Ministan Tinubu ya tayar da kura kan zaben fitar da gwani na gwamna

Fayose ya ce ba a yin adalci wajen zargin shugaban kasa da matsalolin tsaro, alhali gwamnatocin jihohi ya kamata a rika jefa wa tambayoyi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262