Gwamnatin Tarayya Ta ba da Hutun Babbar Sallah, Ta Tura Sako ga Musulmin Najeriya
- Gwamnatin tarayya ta ba da hutun kwanaki biyu ga ma'aikata domin su samu damar gudanar da shagulgulan babbar Sallah ta bana 2026
- Ministan harkokin cikin gida, Dr. Olubunmi Tunji-Oji ya taya daukacin musulmi murnar zagayowar babbar sallah, daya daga cikin ibadun addinin musulunci
- Gwamnatin tarayya ta kuma buƙaci ‘yan Najeriya su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a da nazari domin neman shiriyar Allah ga Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranaku biyu a matsayin hutun Babbar Sallah (Eid al-Adha) ta shekarar 2026.
Gwamnatin ta bayyana ranakun Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 ga Mayu, 2026, a matsayin ranakun hutun ga ma'aikata domin bikin sallar layya watau Eid al-Adha na bana a Najeriya.

Source: Twitter
An ba da hutun babbar sallah a Najeriya
Rahoton Vanguard ya ruwaito cewa Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar yau Litinin, 25 ga watan Mayu, 2027.
Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, ce ta sanya wa hannu a jikin sanarwar a madadin Dr. Tunji Ojo.
Sanarwar ta ce gwamnatin Najeirya ta ba da wannan hutun domin nuna girmamawar ta ga addini da al’adun miliyoyin Musulman Najeriya da ke haɗuwa da sauran Musulmi a duniya wajen gudanar da wannan ibada.
Gwamnatin tarayya ta taya musulmi murna
Dr. Tunji-Ojo ya miƙa saƙon taya murna a madadin gwamnatin tarayya ga dukkan Musulmai a Najeriya da ma waɗanda ke ƙasashen waje.
Bugu da kari, ministan ya bayyana Babbar Sallah a matsayin biki mai matuƙar muhimmanci da ya samo asali daga sadaukarwa, biyayya ga Allah da kuma tausayi ga al’umma.
Gwamnatin tarayya ta kuma buƙaci ‘yan Najeriya su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a da nazari domin neman shiriyar Allah ga ƙasa yayin da take ci gaba da ƙoƙarin samar da zaman lafiya, tsaro da ci gaba ga kowane ɗan ƙasa.
“Sakamakon 'yan uwanta, haɗin kai da kuma ƙaunar juna ne gwamnatin tarayya ke yi wa dukkan Musulmai fatan yin shagulgulan Babbar Sallah cikin kwanciyar hankali, albarka da farin ciki,” in ji sanarwar.
A ranar Laraba, 27 ga watan Mayu, 2026, daidai da 10 ga watan Zul-Hijjah, 1446AH, musulmin Najeriya za su gudanar da babbar sallah ta bana.
A wani rahoton, kun ji cewa
Asali: Legit.ng

