Gwamnatin Katsina Ta Yi Magana kan 'Hadimin Gwamna' da Ake Zargi da Hannu a Garkuwa da Mutane
- Gwamnatin Katsina ta ce ta jima da sallamar Nura Aliyu Garwa daga mukaminsa na mai taimaka wa gwamna kan harkokin ci gaban al’umma
- Ana zargin tsohon hadimin gwamnan da alaka da wata kungiyar masu garkuwa da mutane da ake zargin ta sace yaro dan shekara takwas
- Gwamna Dikko Radda ya nuna takaicinsa kan yadda tsohon hadiminsa ya shiga irin wadannan zarge-zarge, ya kuma yabi yan sanda
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Katsina, Nigeria - Gwamnatin jihar Katsina ta yi karin haske kan zargin da ake yi wa Nura Aliyu Garwa, Babban Mataimaki na Musamman (SSA) ga Gwamna Dikko Radda kan harkokin ci gaban al’umma.
Ana zargin hadimin gwamnan na cikin jagororin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ake alaƙanta ta da satar wani yaro ɗan shekara takwas a cikin birnin Katsina.

Source: Facebook
Dikko ya jima da sallamar Nura Garwa
Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnatin Katsina ta bayyana cewa Gwamna Dikko Radda ya jima da dakatar da Nura Garwa daga mukaminsa bisa wannan zargi da ake masa na hannu a garkuwa da karamin yaro.
Hakan na kunshe ne a a wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Bala Salisu Zango, ya fitar ranar Litinin, 25 ga watan Mayu, 2026.
Gwamnatin ta ce an dakatar da Garwa ne bisa zargin karkatar da kayan tallafi da aka ware domin raba wa mutanen Ƙaramar Hukumar Batsari ƙarƙashin shirin ci gaban al’umma na jihar Katsina
Sanarwar ta ƙara da cewa Garwa daga baya ya nuna sha’awar tsayawa takarar kujerar majalisar dokokin Jihar Katsina domin wakiltar Ƙaramar Hukumar Batsari.
Sai dai gwamnatin ta bayyana cewa Gwamna Radda ya nuna takaici da damuwa kan zargin da ake masa, yana mai cewa abin takaici ne yadda mutum mai matsayi a gwamnati da kuma burin siyasa zai iya shiga irin waɗannan zarge-zarge.
Haka kuma, gwamnan ya yaba wa rundunar yan sandan Katsina da sauran hukumomin tsaro bisa ƙoƙarinsu wajen yaƙi da rashin tsaro da kuma ci gaba da gudanar da ayyukan daƙile laifuffuka.
A baya-bayan nan ne rundunar ‘yan sandan Katsina ta bayyana wasu mutane da ake zargi da hannu a ayyaukan wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane.
Ana zargin kungiyar da satar wani yaro ɗan shekara takwas a unguwar Sardauna Estate da ke cikin birnin Katsina, inda aka ce tsohon hadimin gwamnan na daga cikin waɗanda ake zargi.
Lamarin ya jawo damuwa matuƙa a tsakanin al’umma sakamakon yadda ake zargin wani tsohon jami’in gwamnati da hannu a ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane.
Asali: Legit.ng

