"A Kula": Saudiyya Ta Gargadi Mahajjata kan Aikin Hajjin Shekarar 2026
- Mahajjata daga kasashe daban-daban na duniya na ci gaba da gudanar da aikin hajjin shekarar 2026 a kasa mai tsarki watau Saudiyya
- Hukumar kula da yanayi ta kasar Saudiyya ta bukaci mahajjata da su bi a hankali kam yanayin zafi, inda ta ba su shawarwarin matakan da ya kamata su dauka
- An bukaci mahajjata da su rika yawo da laima domin kaucewa shan zafin rana yayin da suke zirga-zirga wajen gudanar da aikin hajji
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Makkah, kasar Saudiyya - Hukumar kula da yanayi ta kasar Saudiyya ta gargaɗi mahajjata masu halartar aikin hajin shekarar 2026.
Hukumar ta gargadi mahajjata da su shirya wa matsanancin yanayin zafi, inda ake sa ran yanayin zafin zai tashi har zuwa digiri 47 na ma'aunin Celsius a lokacin gudanar da aikin hajjin.

Source: Facebook
Hukumomi a Saudiyya sun ja kunnen mahajjata
Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto a ranar Laraba, 20 ga watan Mayun 2026 cewa hukumar ta buƙaci mahajjata da su ɗauki matakan kariya domin kauce wa rukunonin cututtuka da zafi ke haifarwa.
Hukumar ta bukaci su dauki matakan ne musamman a lokacin gudanar da ayyukan ibada na fili a Makkah da sauran wurare masu tsarki da ke kewaye, jaridar The Islamic Information ta kawo rahoton.
Bisa ga shawarwarin da aka bayar, an ƙarfafa gwiwar mahajjata da su riƙa ɗaukar laima yayin zirga-zirga tsakanin wurare daban-daban, kuma su riƙa shan ruwa akai-akai domin jikinsu kada ya bushe.
An ba mahajjata shawarar matakan dauka
Hukumomin sun kuma shawarci mahajjata da su guji daɗewa a ƙarƙashin hasken rana kai-tsaye a lokutan da zafi ya fi tsananta da rana, kuma su bi umarnin kiwon lafiya da tsaro da jami'an Saudiyya suka bayar a duk tsawon lokacin aikin hajjin.
An kuma yaɗa lambar neman taimakon gaggawa ta Saudiyya, 997, domin mahajjata da ke buƙatar taimakon likita na gaggawa su yi amfani da ita.
Wannan gargaɗi yana zuwa ne yayin da miliyoyin mahajjata daga faɗin duniya ke ci gaba da isa Masarautar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin na shekara-shekara.

Source: Facebook
Karanta wasu labaran kan aikin hajji
- Hajjin 2026: Kasar Saudiyya ta yi gyare gyare, ta tura tallafi ga kasashen Musulmi 27
- Hajjin bana: Wata maniyyaciya daga Najeriya ta rasu 'yan awanni da isa Saudiyya
- Babban jami'i a gwamnatin Bauchi ya rasu a Makkah ana shirin fara aikin hajji
- Dan damfara ya sace wa mahajjaciya 'yar Najeriya daloli a Madina
Mahajjatan Najeriya sun rasu a Saudiyya
A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar kula ta Alhazai ta kasa (NAHCON), ta bayyana mahajjatan da ke fama da rashin lafiya da wadanda suka rasu a kasar Saudiyya.
Hukumar NAHCON ta bayyana cewa akalla mahajjatan Najeriya 54 ne ke kwance a asibitoci a kasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.
Hakazalika, hukumar ta kuma tabbatar da rasuwar mahajjata guda hudu ‘yan Najeriya, wadanda dukkansu mata ne.
Asali: Legit.ng

